Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Gwamnatin  Kano Ta Tura Dalibai 550  Domin Taimakawa Wajen Faɗaɗa Rajistar Katin Zaɓe A Fadin Jihar ‎
Afrika

Gwamnatin  Kano Ta Tura Dalibai 550  Domin Taimakawa Wajen Faɗaɗa Rajistar Katin Zaɓe A Fadin Jihar ‎

April 2, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
IMG 20260402 174619 925

Gwamnatin Jihar Kano ta tura dalibai 550 daga cibiyoyin ilimi tara domin taimakawa wajen faɗaɗa rajistar rajistar masu zaɓe CVR, a wani yunƙuri na ƙara ƙarfafa shiga harkokin dimokuraɗiyya a faɗin jihar.

‎Shugaban Kwamitin Ƙarfafa Rajistar Masu Zaɓe na Jihar Kano, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, ne ya bayyana hakan yayin ƙaddamar da shirin a filin wasanni  na Kofar Mata, inda ake gudanar da babban aikin rajistar masu zaɓe.

‎Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Abbas Ibrahim, Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai, ya fitar a madadin Kwamitin Ƙarfafa Rajistar Masu Zaɓe na Jihar Kano.

‎A cewar Waiya, an horas da daliban domin su taimaka wajen yin rajista ta yanar gizo (online pre-registration), domin rage cunkoso da kuma hanzarta aikin rajistar kai tsaye, musamman ga ɗalibai da sauran al’umma da ke fuskantar matsalar isa cibiyoyin rajista.

‎Ya ƙara da cewa daga cikin daliban, 100 sun fito ne daga Kwalejin Ilimi ta Sa’adatu Rimi, yayin da sauran cibiyoyi takwas suka samar da dalibai 50 kowacce.

‎Waiya, wanda kuma shi ne Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, ya jaddada cewa rajistar masu zaɓe muhimmin hakki ne na ɗan ƙasa, wanda ke taka rawa wajen tabbatar da dimokuraɗiyya mai inganci.

‎Ya ce: “Wannan wata dama ce ga matasa su bayar da gudunmawa wajen gina dimokuraɗiyya. Jajircewarku da gaskiyarku za su taimaka wajen tabbatar da cewa an samu cikakken wakilci a tsarin shugabanci.”

‎Ya kuma buƙaci daliban da su gudanar da aikinsu da gaskiya da riƙon amana, tare da bin ƙa’idojin da aka shimfiɗa, yana mai gargadin su guji duk wani abu da zai kawo tarnaki ga sahihancin aikin.

‎A wani ɓangare kuma, ya bayyana cewa za a karrama daliban da suka fi ƙwazo da nuna nagarta wajen gudanar da aikinsu, domin ƙarfafa gasa mai kyau da kuma ɗaukar nauyi.

‎Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta taka muhimmiyar rawa wajen horas da daliban kan fannoni na fasaha da ɗabi’a da suka shafi rajistar masu zaɓe.

‎Haka kuma, shugabannin cibiyoyin ilimin da abin ya shafa sun halarci wajen ƙaddamar da shirin domin sanya ido, lamarin da ke nuna cikakken goyon bayan hukumomi ga shirin da kuma muhimmancin rawar da matasa ke takawa.

‎Wasu daga cikin daliban da aka zaɓa sun bayyana shirinsu na yin aiki tukuru domin tabbatar da nasarar shirin, tare da jaddada aniyarsu ta taimakawa wajen ƙara yawan masu rajista a jihar.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

‘Ba zan ba ‘yan Najeriya kunya ba’ – Shugaba Tinubu

April 17, 2026

Wannan ce takarata ta ƙarshe – Atiku

April 15, 2026

Shekaru 12 bayan sace ƴan matan Chibok

April 15, 2026

Tsagin ADC ƙarƙashin David Mark ya kori Nafiu Bala da wasu bisa zargin yi wa jam’iyya zagon-ƙasa

April 15, 2026

Hukumomin yaƙi da cin hanci ba su taɓa gayyata ta ba — Pantami

April 14, 2026

An kama jami’an ƴansanda 6 tare da wasu mutane 3 bisa zargin ƙwace da satar mutane a Edo 

April 14, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

By WafsymApril 2, 2026

A Jihar Kano, ana ci gaba da nuna damuwa kan yadda wasu masu anfani da…

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.