Hukumar Shirya Jarabawar Ƙasashen Yammacin Afirka, West African Examinations Council (WAEC), ta bayyana cewa an gudanar da jarabawar ta a cibiyoyi 166 a faɗin Najeriya tsakanin ranar 28 ga Janairu zuwa 14 ga Fabrairu, 2026.
A cikin sanarwar da mukaddashin shugaban hulɗa da jama’a na hukumar, Moyosola F. Adesina, ya fitar daga hedikwatar WAEC da ke Yaba, an ce jimillar ɗalibai 10,480 ne suka zauna jarabawar.
2026: WAEC ta fitar da sakamakon jarrabawar WASSCE na kwamfuta
Daga cikin wannan adadi, ɗalibai 3,429, wanda ya kai kashi 32.72 cikin ɗari, sun samu sakamakon credit a aƙalla darussa biyar ciki har da Turanci da Lissafi—abin da ke nuna ƙaruwa da kashi 5.76 idan aka kwatanta da sakamakon shekarar 2025 da ya tsaya a kashi 26.96.
Hukumar ta kuma bayyana cewa ɗalibai 43 masu buƙata ta musamman sun shiga jarabawar, inda aka ba da kulawa ta musamman ga makafi 11, masu matsalar ji guda 4, da kuma albinos guda 4, a wani yunƙuri na tabbatar da daidaito a fannin ilimi.
Dangane da sakamakon, WAEC ta ce an riga an kammala duba sakamakon ɗalibai 8,418, wanda ya kai kashi 80.32 cikin ɗari, yayin da sakamakon ɗalibai 2,062 ke ci gaba da dubawa sakamakon wasu kurakurai da aka gano daga ɓangaren ɗaliban.
Sai dai hukumar ta riƙe sakamakon ɗalibai 75 bisa zargin hannu a magudin jarabawa, inda ta ce ana ci gaba da bincike kafin ɗaukar matakin da ya dace.
A ƙarshe, WAEC ta shawarci ɗalibai da su duba sakamakonsu ta shafin yanar gizon hukumar, inda kuma za su iya sauke kwafin takardar shaidarsu ta dijital cikin sauƙi.

