Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Tsohon Gwamna Na Fuskantar Bincike Kan Zargin Hannu a Shirin Juyin Mulki
Afrika

Tsohon Gwamna Na Fuskantar Bincike Kan Zargin Hannu a Shirin Juyin Mulki

October 20, 2025
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
Tinubu

Rahotanni sun bayyana cewa tsohon gwamna daga wani yanki na kudu na ƙasar nan wanda ba’a bayyana sunan sa ba, na fuskantar bincike kan zargin cewa yana da alaƙa da wasu jami’an soja da ake tsare da su bisa zargin shirin juyin mulki.

Majiyoyi sun shaida wa Daily Trust cewa ana zargin tsohon gwamnan da taimaka wa da kuɗi wajen shirya juyin mulkin da aka ce an tsara shi a gudanar ranar 25 ga Oktoba.

Takardar Sakandire Ta Isa Bayar Da Damar Rike Mukamin Siyasa — Shehu Sani

Rahotanni daga wasu kafafen labarai sun ce jami’an da ake tsare da su ciki har da Brigediya Janar, Kanal, da wasu duk suna ƙarƙashin ofishin mai ba wa shugaban shawara kan harkokin tsaro na ƙasa (ONSA).

Wata majiya ta tabbatar cewa bincike yana gudana karkashin Hukumar Leken Asirin Soji (DIA), tare da wakilai daga dukkan rundunonin sojoji.

Sai dai Hedikwatar Tsaro ta ƙaryata rahotannin, inda ta ce ta kama jami’an ne saboda “saɓa ƙa’idojin aiki” ba wai saboda yunkurin juyin mulki ba.

DHQ ta ce rahoton juyin mulki karya ne, kuma ta tabbatar da cewa rundunar sojin Najeriya tana nan da cikakken biyayya ga kundin tsarin mulki da gwamnatin shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu.

Majiyoyi daga Nasarawa sun bayyana cewa ɗaya daga cikin jami’an da ake bincike ɗan wani tsohon gwamna ne, kuma iyalinsa sun bayyana damuwa kan lamarin.

A halin yanzu, an ce ana sa ido kan wasu ‘yan siyasa daga arewa da kudu bisa yiwuwar suna da hannu a lamarin.

Featured gwamna juyin mulki
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Wannan ce takarata ta ƙarshe – Atiku

April 15, 2026

Shekaru 12 bayan sace ƴan matan Chibok

April 15, 2026

Hukumomin yaƙi da cin hanci ba su taɓa gayyata ta ba — Pantami

April 14, 2026

An kama jami’an ƴansanda 6 tare da wasu mutane 3 bisa zargin ƙwace da satar mutane a Edo 

April 14, 2026

Maki shida ne ya rage tsakanin Arsenal da Man City

April 13, 2026

Mutane sama da 50 sun rasu a kuskuren harin sojin sama a kasuwa

April 13, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

By WafsymApril 2, 2026

A Jihar Kano, ana ci gaba da nuna damuwa kan yadda wasu masu anfani da…

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.