Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Hatsaniyar data Faru a Karamar Hukumar Rano wadda ta kai ga Rasuwar DPO da wani mutum daya– ‘Yan sanda Sun Nemi Hadin kai don Dawo da Tsaro a Yankin
Labaran Cikin Gida

Hatsaniyar data Faru a Karamar Hukumar Rano wadda ta kai ga Rasuwar DPO da wani mutum daya– ‘Yan sanda Sun Nemi Hadin kai don Dawo da Tsaro a Yankin

May 27, 2025
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
Nig Police force

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta tabbatar da aukuwar wani mummunan lamari a ranar 25 ga Mayu, 2025, da misalin karfe 8:15 na dare a karamar hukumar Rano, inda aka kama wani mai gyaran babur mai suna Abdullahi Musa, ɗan asalin Rano, bisa zargin tuƙin babur cikin haɗari da kuma yiwuwar kasancewa cikin maye, bayan korafe-korafe daga jama’a.

Bayan an tsare shi, sai ya fara nuna alamun rauni, wanda ya sa aka garzaya da shi Asibitin Gwamnati na Rano, inda ya rasu a safiyar ranar 26 ga Mayu, 2025, da misalin karfe 6:00 na safe yayin da ake kula da lafiyarsa.

Biyo bayan rasuwar tasa, wasu fusatattun matasa suka kai farmaki ofishin ‘yan sanda na Rano, tare da kone wani sashi na ofishin da motoci guda biyu, suka lalata wasu motoci goma (10), sannan suka jikkata DPO mai kula da ofishin. An garzaya da DPO ɗin zuwa Asibitin Koyarwa na Aminu Kano, inda daga bisani ya rasu yana karɓar kulawa.

Rundunar Yan sandan ta Kuma ce ta kama mutane ashirin da bakwai (27) da ake zargi da hannu a wannan ta’asa. An kwantar da tarzomar, kuma an dawo da zaman lafiya da doka a yankin.

Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Kano, CP Ibrahim Bakori, PhD, ya kai ziyara wurin da lamarin ya faru, sannan ya kai gaisuwar ta’aziyya ga Mai Martaba Sarkin Rano, Ambasada Dakta Mohammed Isah Umar (Autan Bawo 19). Ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike domin gano musabbabin lamarin da daukar matakin doka kan duk wanda aka samu da laifi.

Hukumar ‘yan sanda ta Jihar Kano na jajantawa iyalan marigayi DPO, wanda ya rasa rayuwarsa a bakin aiki, tare da roƙon jama’a da su kwantar da hankalinsu, su guji ɗaukar doka a hannunsu, su kuma bai wa hukuma hadin kai wajen gudanar da bincike cikin kwanciyar hankali.

Hukumar na tabbatar da kudirinta na ci gaba da tabbatar da zaman lafiya da doka a jihar, tare da neman goyon bayan al’umma a wannan lokaci.

Featured
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Gwamna Abba Ya Kaddamar da Kwamitin Yaƙi da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi, Ya Sanya Hannu Kan Dokar Daba A Kano

July 22, 2026

“Rikicin Shaidar Zama Ɗan Ƙasa a Jos North Ya Ɗauki Sabon Salo, Sarakunan Gargajiya Sun Nemi Shiga Cikin Shari’a.”

July 11, 2026

Sahihin ‎Labari Ke Tabbatar Da Amincewar Jama’a, Ba Gaggawar Wallafa Ba- Shugaban NUJ

July 1, 2026

NWUK Expels 34 Students Over Examination Malpractice

June 30, 2026

Gwamnatin Kano Ta Yi Alƙawarin Ƙara Wa NDLEA Motoci Don Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ‎

June 29, 2026

NDLEA Ta Kone Tan 12.2 Na Miyagun Ƙwayoyi a Kano, Ta Kama Mutum 

June 29, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Gwamnatin Kano Ta Yi Alƙawarin Ƙara Wa NDLEA Motoci Don Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ‎

June 29, 20267

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.