Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Gyara matatar man fetur ta Warri zai kara wa ‘yan Nijeriya ƙwarin gwiwa kan alƙawuranmu – Bola Tinubu
Afrika

Gyara matatar man fetur ta Warri zai kara wa ‘yan Nijeriya ƙwarin gwiwa kan alƙawuranmu – Bola Tinubu

December 31, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayyana matukar farin cikinsa bisa sake bude matatar man fetur ta garin Warri da Kamfanin Mai na Ƙasar NNPCL ya yi a ranar Litinin, inda ya bayyana hakan a matsayin wata gagarumar nasara a shekarar 2024 da ta ƙarawa ‘yan Nijeriya samun fatan alheri a gwamnatinsa.

A ranar Litinin ne, matatar mai ta Warri ta koma aiki makonni bayan kamfanin NNPCL ya sake fara aikin tace gangar danyen fetur 60,000 a kowace rana a matatar Port Harcourt a watan Nuwamba.

Gwamnatin Nijeriya ta ce a ranar Litinin ta koma wasu ayyuka a matatar mai ta Warri bayan rufe ta na tsawon kusan shekaru goma.

A saƙon da ya fitar bayan sanar da sake bude matatar da aka gyara, Shugaba Tinubu cikin kwarin gwiwa ya ce matatar mai ta Warri wadda yanzu tana aiki da kashi 60% cikin 100, na ba da tabbacin cewa shirin gwamnatinsa na ingancin makamashi da tsaro gaba daya suna kan hanya.

Ya kuma yaba wa mahukuntan NNPC karkashin jagorancin Mele Kyari kan yadda suke aiki tukuru domin dawo da martabar Nijeriya a matsayin babbar kasa mai arzikin man fetur.

“Na yi farin ciki da cewa kamfanin NNPCL yana aiwatar da umarnina na maido da dukkan matatun manmu guda hudu zuwa kyakkyawan yanayin aiki.

“Gyaran matatar mai ta Warri a yau ya sanya ni farin ciki ni da ‘yan Nijeriya. Wannan abu zai kara karfafa fata da bai wa ‘yan Nijeriya ƙwarin gwiwa na samun makoma mai kyau na alkawuran da muka yi musu.

“Wannan ci gaban wata babbar hanya ce ta rufe wannan shekara bayan wannan aikin da aka yi musamman idan aka hada da gyara tsohuwar matatar Port Harcourt da aka yi duk cikin shekarar nan.

Tun da fari gwamnati ta yi alkawarin farfado da matatun man da suka lalace saboda rashin kulawa.

Mele Kyari, shugaban kamfanin man fetur na kasa NNPC, a lokacin da ya ziyarci cibiyar tare da jami’an gwamnati, da da ‘yan jarida ya ce, “Wannan kamfanin yana aiki a yanzu. Ba mu kammala shi 100 bisa 100 ba.

Featured
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Yawan Al’umma Na Iya Tsananta Matsalar Tsaro a Nijeriya-Bankin Duniya

October 20, 2025

Tsohon Gwamna Na Fuskantar Bincike Kan Zargin Hannu a Shirin Juyin Mulki

October 20, 2025

Kano: KIRS Ta Fitar Da Sabon Tsarin Biyan Haraji Ta Hanyar Fasahar Zamani

October 6, 2025

Takardar Sakandire Ta Isa Bayar Da Damar Rike Mukamin Siyasa — Shehu Sani

October 6, 2025

Kwalara ta kashe mutane 4,778 a Najeriya tsakanin shekarar 2020 zuwa 2024

October 6, 2025

NDLEA ta kama tarin ƙwayoyi da ake shirin safararsu zuwa Birtaniya

October 6, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsohon Gwamna Na Fuskantar Bincike Kan Zargin Hannu a Shirin Juyin Mulki

By WafsymOctober 20, 2025

Rahotanni sun bayyana cewa tsohon gwamna daga wani yanki na kudu na ƙasar nan wanda…

Hawan Jini: Ƙungiyoyi Sun Yi Gargadi Kan Yaduwar Cutar a Nijeriya

September 27, 2025

Barkewar Cututtuka Uku Sun Tayar da Hankalin Hukumomin Lafiya a Nijeriya ‎

September 27, 2025

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

April 13, 2025
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.