Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Gwamna Abba Ya Kaddamar da Kwamitin Yaƙi da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi, Ya Sanya Hannu Kan Dokar Daba A Kano
Babban Labari

Gwamna Abba Ya Kaddamar da Kwamitin Yaƙi da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi, Ya Sanya Hannu Kan Dokar Daba A Kano

July 22, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
IMG 20260722 WA0020

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya ƙaddamar da Kwamitin Haɗin Gwiwa na Hukumomi kan Yaƙi da Shan Miyagun Ƙwayoyi, tare da sanya hannu kan Dokar Zartarwa da za ta ƙarfafa yaƙi da daba da sauran ayyukan ta’addanci a faɗin jihar.

Mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba.

Sakamakon Binciken Jami’ar Northwest Kano Ya Haskaka Matsalolin Lafiyar Al’umma a Tofa

Gwamna Abba ya ce shan miyagun ƙwayoyi na daga cikin manyan matsalolin da ke addabar matasan Kano, yana mai cewa matsalar tana haddasa aikata laifuka, rusa zaman lafiyar iyalai, raunana tattalin arziki da kuma kawo cikas ga zaman lafiya a cikin al’umma.

Ya bayyana cewa sabon kwamitin zai haɗa kai da hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki wajen tattara bayanan sirri, aiwatar da doka, wayar da kan jama’a, da kuma kula da masu fama da shaye-shaye domin rage yaɗuwar matsalar.

Gwamnan ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar za ta samar wa kwamitin isassun kuɗaɗe, motocin aiki, ofisoshi, kayan aiki da kuma kariyar jami’an tsaro domin sauƙaƙa masa gudanar da ayyukansa cikin inganci da ‘yanci.

Ya ƙara da cewa gwamnatinsa ta riga ta kafa cibiyoyin gyaran masu shaye-shaye na maza da mata, tare da alƙawarin ci gaba da faɗaɗa ayyukan gyaran hali da dawo da waɗanda suka kamu da shaye-shaye cikin al’umma.

Dangane da Dokar Zartarwar da ya sanya wa hannu, Gwamna Abba ya ce za ta samar da ingantaccen tsarin doka da zai taimaka wajen tarwatsa ƙungiyoyin daba, dakile tashe-tashen hankula masu alaƙa da siyasa da kuma ƙarfafa ayyukan hukumomin tsaro wajen tabbatar da doka da oda a Kano.

Da yake jawabi bayan ƙaddamar da kwamitin, shugaban kwamitin, Barrista Muhuyi Magaji Rimingado, ya gode wa gwamnan bisa amincewar da ya nuna masa da sauran mambobin kwamitin.

Ya yi alƙawarin gudanar da aikin da aka ɗora musu cikin gaskiya, ƙwarewa da riƙon amana, ba tare da nuna son kai ko sassauci ba.

Muhuyi ya ce kwamitin zai yi aiki tare da hukumomin tsaro, sarakunan gargajiya, shugabannin addini, ƙungiyoyin fararen hula, cibiyoyin ilimi da shugabannin al’umma domin yaƙi da shan miyagun ƙwayoyi da tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa a jihar.

A ƙarshe, Gwamna Abba ya yi kira ga al’ummar Kano da su ba kwamitin haɗin kai ta hanyar bayar da sahihan bayanai ga hukumomin tsaro, yana mai cewa yaƙi da shaye-shaye da daba ba aikin gwamnati kaɗai ba ne, illa haɗin kan kowa da kowa.

Ya bayyana ƙwarin gwiwar cewa haɗa Dokar Zartarwar da ayyukan sabon kwamitin zai taimaka wajen rage laifukan da ke da alaƙa da miyagun ƙwayoyi, tare da samar da Jihar Kano mai zaman lafiya da tsaro.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

“Rikicin Shaidar Zama Ɗan Ƙasa a Jos North Ya Ɗauki Sabon Salo, Sarakunan Gargajiya Sun Nemi Shiga Cikin Shari’a.”

July 11, 2026

Sarkin Gaya: Mallakar Katin Zaɓe Shi Ne Ginshiƙin Zaɓen Shugabanni Nagari

July 3, 2026

Sahihin ‎Labari Ke Tabbatar Da Amincewar Jama’a, Ba Gaggawar Wallafa Ba- Shugaban NUJ

July 1, 2026

NWUK Expels 34 Students Over Examination Malpractice

June 30, 2026

Gwamnatin Kano Ta Yi Alƙawarin Ƙara Wa NDLEA Motoci Don Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ‎

June 29, 2026

NDLEA Ta Kone Tan 12.2 Na Miyagun Ƙwayoyi a Kano, Ta Kama Mutum 

June 29, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Gwamnatin Kano Ta Yi Alƙawarin Ƙara Wa NDLEA Motoci Don Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ‎

June 29, 20267

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.