Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Kwamitin Kartakwana a kan Katin Zaɓe Ya Nemi Limaman Juma’a Su Wayar da Kan Jama’a a Kano
Uncategorized

Kwamitin Kartakwana a kan Katin Zaɓe Ya Nemi Limaman Juma’a Su Wayar da Kan Jama’a a Kano

June 25, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
IMG 20260625 WA0019

‎Kwamitin Kartakwana a kan Katin Zaɓe (CVR) a Jihar Kano ya buƙaci limaman masallatan Juma’a da su ƙara himma wajen wayar da kan al’umma kan muhimmancin mallakar katin zaɓe da kuma shiga cikin harkokin dimokuraɗiyya.

‎Wannan kira ya fito ne yayin wata ganawa da kwamitin ya yi da limaman masallatan Juma’a, inda Shugaban Ƙaramin Kwamitin Hulɗa da Malamai, Sheikh Ibrahim Abubakar Tofa, ya jaddada muhimmancin rawar da malamai ke takawa wajen isar da saƙonnin da suka shafi ci gaban al’umma.

‎Sheikh Ibrahim Abubakar Tofa ya bayyana cewa malamai na da tasiri mai girma a cikin al’umma, don haka haɗin gwiwarsu zai taimaka wajen ƙarfafa jama’a su fito su yi rajista tare da sabunta katin zaɓensu kafin wa’adin da Hukumar Zaɓe ta ƙasa (INEC) ta gindaya.

‎A nasa jawabin, Shugaban Kwamitin na Jiha kuma Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kano, Comrade Ibrahim Abdullahi Waiya, wanda Comrade Abbas Ibrahim ya wakilta, ya ce limaman Juma’a na daga cikin manyan ginshiƙan wayar da kan jama’a kan batutuwan da suka shafi ci gaban al’umma da ƙarfafa dimokuraɗiyya.

‎Ya ce kwamitin ya yi amanna cewa saƙonnin da limamai ke isarwa daga mimbari za su taimaka wajen ƙara yawan masu rajistar zaɓe, musamman matasa da mata, domin tabbatar da cewa kowa ya samu damar amfani da haƙƙinsa na zaɓe.

‎Wakilin shugaban kwamitin ya kuma yi kira ga al’ummar jihar da su rungumi shirin sabunta rajistar zaɓe tare da tabbatar da cewa sun mallaki katin zaɓensu, yana mai cewa katin zaɓe wata muhimmiyar hanya ce ta zaɓar shugabanni nagari da kuma tabbatar da ci gaban dimokuraɗiyya.

‎Ya ƙara da cewa kwamitin zai ci gaba da gudanar da shirye-shiryen wayar da kai a sassa daban-daban na jihar domin tabbatar da cewa saƙon muhimmancin katin zaɓe ya isa ga kowane ɗan ƙasa da ya cancanci yin zaɓe.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Ranar Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi ta Duniya: Ƙungiyoyi Sun Yi Gangamin Wayar da Kai, Sun Nemi Haɗin Kan Al’umma Don Daƙile Shaye-shaye a Kano

June 26, 2026

Majalisa ta buƙaci a dakatar da yaƙin neman zaɓe a jihohin arewa 8 saboda matsalar tsaro

April 24, 2026

Hon.Sha’aban ya jaddada janye neman takarar Sanatan Kaduna ta Arewa, tare da bayyana goyon duk wanda APC ta tsayar 

April 21, 2026

Kotu ta bayar da sammacin kama tsohuwar ministan Buhari Sadiya Faruk bisa zargin badakalar kudade

April 17, 2026

Shekaru 12 bayan sace ƴan matan Chibok

April 15, 2026

Amurka ta dakatar da bayar da bizarta a Abuja

April 10, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Gwamnatin Kano Ta Yi Alƙawarin Ƙara Wa NDLEA Motoci Don Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ‎

June 29, 20267

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.