Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Majalisa ta buƙaci a dakatar da yaƙin neman zaɓe a jihohin arewa 8 saboda matsalar tsaro
Uncategorized

Majalisa ta buƙaci a dakatar da yaƙin neman zaɓe a jihohin arewa 8 saboda matsalar tsaro

April 24, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
5941ed9c 2e95 4186 a207 14ea59caea07.jpg

Majalisar dattawan Najeriya ta buƙaci gwamnatin ƙasar ta duba yiwuwar dakatar da yaƙin neman zaɓen 2027 a wasu jihohin arewa guda takwas da ke fama da matsalar tsaro.

Sanata mai wakiltar Bauchi ta tsakiya Abdul Ningi ne ya gabatar da ƙudurin a zaman majalisar na ranar Alhamis, inda ya ce akwai buƙatar a duba yanayin tashe-tashen hankulan da ake fama da su a ƙasar.

Kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito, Ningi ya ce bai kamata ƴan majalisar su kauda kai daga matsalar tsaron da ke damun wasu sassan ƙasar saboda su suna zaune a Abuja.

“Mataki ne da ya zama wajibi mu ɗauka. Ko dai a dakatar da duk wasu tarukan siyasa a faɗin ƙasar ko kuma a dakatar a jihohin da ke da matsala,” in ji Sanata Ningi.

Sanatan ya lissafo johohin Borno, Plateau, Bauchi, Benue, Niger, Sokoto, Kebbi da wasu sassan Kano.

“Ya kamata mu dakatar da duk wasu abubuwan siyasa a waɗannan jihohin har sai lamuran tsaro sun daidaita,” in ji shi.

Gargaɗin na Sanata Ningi na zuwa ne a daidai lokacin da ake samun ƙaruwar hare-haren Boko Haram a yankin Arewa Maso Gabashin Najeriya, ciki har da hare-hare kan sansanonin soji a ƙasar da kuma garkuwa da mutane.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Hon.Sha’aban ya jaddada janye neman takarar Sanatan Kaduna ta Arewa, tare da bayyana goyon duk wanda APC ta tsayar 

April 21, 2026

Kotu ta bayar da sammacin kama tsohuwar ministan Buhari Sadiya Faruk bisa zargin badakalar kudade

April 17, 2026

Shekaru 12 bayan sace ƴan matan Chibok

April 15, 2026

Amurka ta dakatar da bayar da bizarta a Abuja

April 10, 2026

Kano, Sokoto da jihohi tara na iya fuskantar ɓarkewar cutar sankarƙau – NiMet

March 14, 2026

Ayyuka Takwas Masu Tarin Lada A Kwanaki 10 Na Ƙarshen Watan Ramadan

March 13, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.