Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Hon.Sha’aban ya jaddada janye neman takarar Sanatan Kaduna ta Arewa, tare da bayyana goyon duk wanda APC ta tsayar 
Uncategorized

Hon.Sha’aban ya jaddada janye neman takarar Sanatan Kaduna ta Arewa, tare da bayyana goyon duk wanda APC ta tsayar 

April 21, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
IMG 20260421 WA0009

Hon.Sha’aban ya jaddada janye neman takarar Sanatan Kaduna ta Arewa, tare da bayyana goyon duk wanda APC ta tsayar

Cikin wata sanarwa da Iyalan Hon. Sani Sha’aban, Danburan Zazzau kuma Barden Keffi, suka fitar dauke da sanya hannun Alhaji Ahmad Bamalli ta bayyana cewar bisa wasu dalilai bayan shawarwarin da aka tattauna daga wannan rana ta Talata 21/4/2026 muna sanar da dukkannin magoya bayan Hon. Sani Sha’aban cewar ya janye daga neman takarar kujerar Sanata a Shiyyar Kaduna ta Arewa wato (zone one), tare da bayyana goyon baya ga duk dan takarar da APC ta tsayar.

A cikin sanarwar an bayyana cewa an dauki wannan mataki ne na janye tamarar ne daga ne bisa la’akari da muradun iyalansa.

Sanarwar ta ce: “Hon. Sha’aban yana nan daram kan wannan matsaya, kuma ba zai nemi wata kujera ta siyasa a jihar ba. Har ila yau, zai cigaba da biyayya ga jam’iyyar APC, kuma a shirye yake ya bayar da gagarumar gudunmawa domin samun nasarar APC a Jihar Kaduna da ma Najeriya baki daya.”

Sanarwar ta kuma kara da cewa Hon. Sha’aban ya yi alkawarin bayar da cikakken goyon baya ga duk wanda jam’iyyar ta tsayar a matsayin dan takara a kowacce kujera a Jihar Kaduna dama kasa baki daya.

Haka kuma, sanarwar ta yi kira ga dukkan magoya bayan Sha’aban, mambobin jam’iyya, da al’ummar Kaduna ta Arewa da su mutunta tare da fahimtar wannan mataki, yana mai nuna yadda da duk“abin da Allah Ya kaddara.”

Sanarwar ta nuna godiya ga daukacin al’ummar Jihar Kaduna bisa ci gaba da fatan alheri, addu’o’i, da goyon baya ga Hon. Sani M. Sha’aban.

Ahmad Bamalli ya sanya hannu kan sanarwar a madadin daukacin iyalan Hon. Sani Sha’aban.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Majalisa ta buƙaci a dakatar da yaƙin neman zaɓe a jihohin arewa 8 saboda matsalar tsaro

April 24, 2026

Kotu ta bayar da sammacin kama tsohuwar ministan Buhari Sadiya Faruk bisa zargin badakalar kudade

April 17, 2026

Shekaru 12 bayan sace ƴan matan Chibok

April 15, 2026

Amurka ta dakatar da bayar da bizarta a Abuja

April 10, 2026

Kano, Sokoto da jihohi tara na iya fuskantar ɓarkewar cutar sankarƙau – NiMet

March 14, 2026

Ayyuka Takwas Masu Tarin Lada A Kwanaki 10 Na Ƙarshen Watan Ramadan

March 13, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.