Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » El-Rufa’i ya sake zargin yunƙurin kama shi
Afrika

El-Rufa’i ya sake zargin yunƙurin kama shi

April 21, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
mallam nasir el rufai governor of kaduna state nigeria 768x427

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya yi zargin cewa akwai wani sabon shiri na haɗa shi da aikata laifuka domin sake tsare shi.

A wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Muyiwa Adekeye, ya fitar, ya bayyana cewa wannan yunkuri na daga cikin wani tsari na ɓata masa suna da kuma hana shi samun ‘yanci.

Sanarwar ta kuma ce El-Rufai na duba yiwuwar ɗaukar matakin shari’a kan jaridar The Nation, bisa wani rahoto da ta wallafa da ke danganta shi da wani hari da aka kai gidan wani shaida a Kaduna.

Rahoton jaridar ya ambato wani shaida mai suna Mohammed Umar Karage, wanda ya ce wasu ‘yan bindiga sun kai masa hari, tare da hasashen cewa hakan na da alaƙa da shari’ar da yake bayar da shaida a cikinta.

Sai dai ɓangaren El-Rufai ya ƙaryata wannan zargi, yana mai cewa an tsara rahoton ne domin ɓata masa suna da kuma shafar buƙatarsa ta neman beli a kotu.

Sanarwar ta tuno cewa a watan fabrairu, an yi yunkurin kama shi a filin jirgin saman Abuja bayan dawowarsa daga birnin Alkahira, kafin daga bisani ya amsa gayyatar hukumar EFCC, wadda ta tsare shi, sannan aka miƙa shi ga ICPC.

Tsohon gwamnan ya ce shi ɗan ƙasa ne mai bin doka, kuma ba shi da wata alaƙa da harin da ake zargi, yana mai jaddada cewa za su ɗauki matakin shari’a kan duk wani abin da ya shafi ɓata masa suna.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Rikicin ACF: Lokaci Ya Yi Na Rushe Tsohon Tsari Da Yin Garambawul —Abbas Ibrahim 

May 12, 2026

Za mu mayar da martani kan harin da aka kai wa jirgin ruwanmu – Koriya ta Kudu

May 11, 2026

Dalilin da ya sa na maida akwatin zaɓena Abuja – Pantami

May 11, 2026

Dangote na shirin gina matatar mai a ƙasar Kenya

May 11, 2026

Samar da Aminci, Shi Ne Farko — Dole a Kawar Da Siyasar Dauka Makamai Daga Fagen Siyasar Kano

May 5, 2026

Pantami ya yi watsi da tsarin maslaha bayan kin daukar shi a matsayin dan takarar gwamnan Gombe

May 3, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.