Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar wa da al’ummar Najeriya cewa gwamnatinsa ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen gina ƙasa mai dorewa, zaman lafiya, da wadata. Ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis yayin da ya karɓi baƙuncin tawagar mambobin ƙungiyar Renewed Hope Ambassadors ƙarƙashin jagorancin Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma, a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.
Shugaba Tinubu ya bayyana cewa tsarin siyasa da tattalin arziƙin da suka daɗe suna dakushe ci gaban ‘yan ƙasa, yanzu ana musanya su da sabbin tsare-tsare da za su ba kowa damar cin moriyar arziƙin ƙasa. Ya kuma sha alwashin ci gaba da aiwatar da garambawul ɗin da nufin samar wa talakawa da marasa ƙarfi guraben ayyukan yi da sauƙin rayuwa.
Shekaru 12 bayan sace ƴan matan Chibok
“Kuna wakiltar lamirin al’ummar da ke son kakkabe sarƙar talauci da yanke ƙauna,” in ji shugaban sa’ilin da yake jawabi ga tawagar.
Ya buƙaci ‘yan Najeriya kada su yarda da kalaman ɓata suna na ‘yan hamayya, inda ya ce idan ma ba su ganin ayyukan hanyoyi da gadoji da ake yi, to za a samar musu da gilashin gani don su gani da kyau.
Taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati da na jam’iyya, ciki har da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Farfesa Nentawe Goshwe Yilwatda, Gwamnoni da suka haɗa da na Yobe, Gombe, Kebbi, Ebonyi, Delta, Kogi, Ekiti, Benue, Taraba, Edo, da Kaduna, Tsofaffin Gwamnoni da Shugabannin Majalisa Kamar su Aminu Bello Masari, Ifeanyi Okowa, Tanko Al-Makura, da Anyim Pius Anyim.
A nasa jawabin, tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Aminu Bello Masari, ya yaba wa shugaban bisa ƙarfin halin aiwatar da sauye-sauyen da wasu shugabannin na baya suka kasa yi, musamman batun cire tallafin mai da haɗe farashin canjin kuɗi.
Masari ya tabbatar wa shugaban cewa jiga-jigan siyasar shiyyar Arewa maso Yamma suna bayansa ɗari bisa ɗari, kuma za su zagaya don duba ayyukan da gwamnatin tarayya ke yi a shiyyar domin wayar da kan jama’a.
Daga ƙarshe, Shugaba Tinubu ya buƙaci mambobin ƙungiyar da su ci gaba da isar da saƙon fatan alheri ga jama’a a matakin gundumomi da ƙauyuka, yana mai jaddada cewa “Najeriya tana hannun amintattu.”

