Manchester City ta ƙara rage yawan makin da ke tsakaninta da Arsenal bayan nasarar da ta samu a wasan da ta fafata da Chelsea.
Manchester City ta yi nasara kan Chelsea da ci 0-3 a filin wasa na Stamford Bridge.
Yanzu Manchester City tana da maki 64 a matsayi na biyu, bayan Arsenal da ke ta ɗaya da maki 70.
City na da wasa guda kwantai da Crystal Palace, wanda aka ɗaga yin shi saboda dalilai a baya, idan City ta ci wasan zai zama saura maki 3 kacal tsakaninta da Arsenal.
A yanzu haka kuma a makon gobe ne Arsenal ɗin za ta fafata da City a filin wasa na Etihad da ke Manchester.
Ko da Manchester City ta ci wasan zai zama akwai banbancin kwallo tsakaninta da Arsenal, wanda watakila hakan ya baiwa Gunners damar ci gaba da zama a matsayi na daya a gasar.
Wasa shida ne ya rage wa Arsenal kuma ta ba da tazarar maki shida, yayin da City wasa bakwai ne ya rage mata.
Wannan ne kusan karo na uku da Arsenal ke dadewa a saman teburi amma daf da ƙarshen kaka ta fuskanci koma baya.

