Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Gwamnatin Kano ta musanta hannu a yarjejeniyar fili a makarantar FGC 
Afrika

Gwamnatin Kano ta musanta hannu a yarjejeniyar fili a makarantar FGC 

April 7, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
FB IMG 1775554964168

Gwamnatin Jihar Kano ta musanta zargin cewa tana da hannu a wata yarjejeniyar musayar fili da ake dangantawa da Kwalejin Gwamnatin Tarayya da ke Kano (FGC Kano).

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da sakataren yada labarai na Gwamnan jihar, Mustapha Muhammad, ya fitar a ranar Litinin.

A cikin sanarwar, gwamnatin ta bayyana karara cewa ba ta da hannu a kowace irin yarjejeniya, tattaunawa ko wata alaka da aka yi dangane da wannan fili.

Ta kuma jaddada cewa Kwalejin Gwamnatin Tarayya ta Kano tana karkashin ikon Gwamnatin Tarayya ne ta hannun Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, wadda ita kadai ke da alhakin yanke duk wani hukunci da ya shafi makarantar.

Gwamnatin jihar ta kara da cewa duk wani yunkuri na alakanta gwamnatin ko mukarraban gwamna Abba Kabir Yusuf da wannan zargin ba shi da tushe, kuma y yaudarar jama’a ne.

Duk da amincewa da damuwar da wasu ‘yan kasa suka nuna, gwamnatin ta bukaci kafafen yada labarai da su rika bin ka’idojin gaskiya, adalci da aikin jarida nagari, tare da kaucewa wallafa rahotannin da ba a tabbatar da su ba.

A karshe, gwamnatin ta sake jaddada kudurinta na tabbatar da gaskiya, bin doka da kuma kare muradun jama’a.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

‘Ba zan ba ‘yan Najeriya kunya ba’ – Shugaba Tinubu

April 17, 2026

Wannan ce takarata ta ƙarshe – Atiku

April 15, 2026

Shekaru 12 bayan sace ƴan matan Chibok

April 15, 2026

Tsagin ADC ƙarƙashin David Mark ya kori Nafiu Bala da wasu bisa zargin yi wa jam’iyya zagon-ƙasa

April 15, 2026

Hukumomin yaƙi da cin hanci ba su taɓa gayyata ta ba — Pantami

April 14, 2026

An kama jami’an ƴansanda 6 tare da wasu mutane 3 bisa zargin ƙwace da satar mutane a Edo 

April 14, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

By WafsymApril 2, 2026

A Jihar Kano, ana ci gaba da nuna damuwa kan yadda wasu masu anfani da…

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.