Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Babban Bankin CBN Ya Fitar Da Sunayen Bankuna 33 Da Suka Cika Ƙa’idar Ƙara Jarinsu
Afrika

Babban Bankin CBN Ya Fitar Da Sunayen Bankuna 33 Da Suka Cika Ƙa’idar Ƙara Jarinsu

April 1, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
images

Babban Bankin Najeriya CBN ya fitar da sunayen bankuna 33 da ya amince cewa jarinsu ya kai su ci gaba da gudanar da hada-hada a cikin ƙasar, a wani yunƙuri na kare dukiyoyin abokan hulɗarsu.

Cikin wata sanarwa da CBN ya fitar a jiya Laraba, ya ce shirin wanda aka soma tun watan Maris na shekarar 2024, an kammala shi a yanzu bayan shafe watanni 24 ana yinsa, domin ƙarfafa tsarin hada-hadar kuɗi tsakanin bankuna da abokan hulɗarsu a Najeriya.

Gawuna da Kwankwaso sun hade

Babban bankin ya ce bankunan 33 da aka amince dasu sun samar da jari na Naira tiriliyan 4 da biliyan 650 ƙarƙashin sabon shirin da ya ƙaddamar.

CBN ya ce shirin ya samu karɓuwa sosai a wajen masu zuba jari na cikin gida da kuma waje, inda kashi fiye da 72 na jarin ya zo daga cikin ƙasar, yayin da kashi 27 ya zo daga abokan hulɗa na ƙasashen waje.

Manyan bankuna da suke hada-hada ta ƙasa da ƙasa, sun cika sharaɗin da aka gindaya musu na samun jarin da ya haura Naira biliyan 500, cikinsu akwai bankin GT, da FCMB, da Fidelity, da Zenith, da Access, da Firstbank, da kuma UBA.

To sai dai CBN ya ce zai yi ƙarin bayani game da bankin Polaris da Keystone da kuma Union da a halin yanzu suke kasancewa ƙarƙashin kulawarsa, wanda tunda fari gwamna Olayemi Cardoso ya ce ba lallai su kasance cikin sabon tsarin ba, saboda matsaloli da suke fuskanta.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

‘Ba zan ba ‘yan Najeriya kunya ba’ – Shugaba Tinubu

April 17, 2026

Wannan ce takarata ta ƙarshe – Atiku

April 15, 2026

Shekaru 12 bayan sace ƴan matan Chibok

April 15, 2026

Tsagin ADC ƙarƙashin David Mark ya kori Nafiu Bala da wasu bisa zargin yi wa jam’iyya zagon-ƙasa

April 15, 2026

Hukumomin yaƙi da cin hanci ba su taɓa gayyata ta ba — Pantami

April 14, 2026

An kama jami’an ƴansanda 6 tare da wasu mutane 3 bisa zargin ƙwace da satar mutane a Edo 

April 14, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

By WafsymApril 2, 2026

A Jihar Kano, ana ci gaba da nuna damuwa kan yadda wasu masu anfani da…

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.