Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Gawuna Ya Fice Daga Jam’iyyar APC
Afrika

Gawuna Ya Fice Daga Jam’iyyar APC

March 30, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
FB IMG 1774862969126

Tsohon mataimakin gwamnan Jihar Kano, Nasiru Yusuf Gawuna, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar All Progressives Congress (APC).

A cikin wata takardar murabus mai ɗauke da kwanan watan 29 ga Maris, 2026, wadda ya aikewa shugaban jam’iyyar a mazabarsa ta Gawuna da ke karamar hukumar Nassarawa, Gawuna ya ce matakin da ya dauka na barin jam’iyyar na son rai ne kuma na kashin kansa.

Gawuna ya sauka daga shugabancin kwamitin Gudanarwa na Bankin Lamuni na Tarayya.

Ya bayyana a cikin takardar cewa: “Ina sanar da ku a hukumance cewa na fice daga jam’iyyar APC daga ranar 29 ga Maris, 2026.”

Tsohon mataimakin gwamnan ya kuma gode wa jam’iyyar bisa damar da ta ba shi a lokacin da yake cikinta.

Gawuna, wanda shi ne dan takarar gwamna na APC a zaben 2023 a Kano, bai bayyana inda zai dosa a siyasance ba bayan ficewar tasa.

Ficewar tasa na zuwa ne a lokacin da ake ci gaba da sauye-sauyen siyasa a jihar Kano, gabanin zabukan gaba.

Wasu majiyoyi na kusa da shi sun ce ana sa ran zai gana da tsohon gwamnan jihar, Rabiu Musa Kwankwaso, a daren Litinin a gidansa da ke Miller Road.

 

DAILY NIGERIAN

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

“Rikicin Shaidar Zama Ɗan Ƙasa a Jos North Ya Ɗauki Sabon Salo, Sarakunan Gargajiya Sun Nemi Shiga Cikin Shari’a.”

July 11, 2026

Sarkin Gaya: Mallakar Katin Zaɓe Shi Ne Ginshiƙin Zaɓen Shugabanni Nagari

July 3, 2026

Sahihin ‎Labari Ke Tabbatar Da Amincewar Jama’a, Ba Gaggawar Wallafa Ba- Shugaban NUJ

July 1, 2026

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rushe Tsarin Karatu Mai Dauke Da JSS Da SS A Makarantun Sikandire A Najeriya

June 30, 2026

Jami’ar Northwest Kano Ta Kori Dalibai 34 Saboda Karya Dokokin Jarabawa ‎

June 30, 2026

NWUK Expels 34 Students Over Examination Malpractice

June 30, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Gwamnatin Kano Ta Yi Alƙawarin Ƙara Wa NDLEA Motoci Don Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ‎

June 29, 20267

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.