Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Hisbah ta kama wasu matasa a otel a Kano
Afrika

Hisbah ta kama wasu matasa a otel a Kano

March 27, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
Hukumar Hisbah Haramta Zancen Dare A Mota A Kano (1)

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta ce ta kama wasu matasa 21 a wani otel da ke yankin Kureken Sani a ƙaramar hukumar Kumbotso bisa zargin aikata abubuwan da suka saɓa wa dokokin addini.

Mataimakin Babban Kwamandan hukumar, Dakta Mujahid Aminuddeen, ya tabbatar wa jaridar Daily Trust faruwar lamarin, inda ya ce an kama mata 11, wasu daga cikinsu na da shekaru tsakanin 17 zuwa 25.

Kotu ta ba da umarnin kama shugaban PDP Tanimu Turaki

Ya ƙara da cewa an kama maza 10, mafi yawansu matasa da shekarunsu ba su wuce 30 ba.

A cewarsa, an cafke mutanen ne yayin da ake zargin suna shirya wani taro da ya saɓa wa dokokin Hisbah.

Aminuddeen ya kuma bayyana cewa an kama manajan otel din dangane da wannan lamari.

Ya ce za a gurfanar da waɗanda aka kama a gaban kotu domin fuskantar hukunci daidai da doka.

Haka kuma, ya buƙaci al’umma da su riƙa sanya ido tare da kai rahoton duk wani abu da suke zargi, musamman wanda ya shafi kananan yara, ga hukumomin da suka dace.

Wannan kamen na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan da hukumar ta sanar da kama matasa sama da 600 bisa zargin aikata abubuwan da ba su dace ba a lokacin bukukuwan Sallah da suka gabata.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Rikicin ACF: Lokaci Ya Yi Na Rushe Tsohon Tsari Da Yin Garambawul —Abbas Ibrahim 

May 12, 2026

Za mu mayar da martani kan harin da aka kai wa jirgin ruwanmu – Koriya ta Kudu

May 11, 2026

Dalilin da ya sa na maida akwatin zaɓena Abuja – Pantami

May 11, 2026

Dangote na shirin gina matatar mai a ƙasar Kenya

May 11, 2026

Samar da Aminci, Shi Ne Farko — Dole a Kawar Da Siyasar Dauka Makamai Daga Fagen Siyasar Kano

May 5, 2026

Pantami ya yi watsi da tsarin maslaha bayan kin daukar shi a matsayin dan takarar gwamnan Gombe

May 3, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.