Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » CAF Ta Kwace Kofin AFCON 2025 Daga Senegal, Ta Bai Wa Morocco
Afrika

CAF Ta Kwace Kofin AFCON 2025 Daga Senegal, Ta Bai Wa Morocco

March 18, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
FB IMG 1773791354172

‎Hukumar ƙwallon ƙafa ta Afirka CAF ta kwace kofin zakarun nahiyar Afirka na 2025 daga ƙasar Senegal, tare da bai wa Morocco nasarar zama zakarun gasar.

‎Sanarwar da CAF ta fitar ta ce kwamitin sauraron ƙorafi na hukumar ya yanke hukuncin cewa tawagar Senegal ta karya dokokin gasar, bayan da wasu daga cikin ’yan wasanta suka fice daga filin wasa a yayin wasan ƙarshe domin nuna rashin amincewa da hukuncin alƙali.

‎Gamayyar Ƙungiyoyin APC sun amince da kungiyar Sen Yari The Renewed Hope Network TRN

‎Hukumar ta ƙara da cewa an ayyana Senegal da laifin watsi da wasa, wanda ya sa aka sauya sakamakon wasan daga 1-0 da Senegal ta samu zuwa 3-0 a hukumance domin Morocco.

‎Jaridar Inda Ranka  ta ruwaito cewa wasan ƙarshe na gasar ya gudana ne cikin yanayi mai cike da cece-kuce, musamman a ƙarshen lokaci inda aka bai wa Morocco bugun fenariti bayan duba VAR.

‎Hukuncin ya janyo fushin ’yan wasan Senegal, inda wasu suka dakatar da wasa na wani lokaci, lamarin da ya haifar da tsaiko na kusan mintuna 20.

‎A yayin rikicin, wasu daga cikin magoya bayan Senegal sun yi yunƙurin kutsawa cikin fili, tare da jefa wasu kayayyaki a cikin Filin, kafin jami’an tsaro su shawo kan lamarin.

‎A wasan dai, ɗan wasan Morocco Brahim Diaz ya kasa cin fenaritin, bayan mai tsaron ragar Senegal Edouard Mendy ya tare ƙwallon.

‎Daga baya ne kuma Pape Gueye ya ci ƙwallon da ta bai wa Senegal nasara a lokacin ƙarin lokaci, kafin hukuncin CAF ya soke sakamakon.

‎Hukuncin na CAF na ɗaya daga cikin matakan ladabtarwa da ke haifar da muhawara, musamman duba da yadda wasan ƙarshe ya kasance mai cike da rikice-rikice.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Hukumomin yaƙi da cin hanci ba su taɓa gayyata ta ba — Pantami

April 14, 2026

An kama jami’an ƴansanda 6 tare da wasu mutane 3 bisa zargin ƙwace da satar mutane a Edo 

April 14, 2026

Maki shida ne ya rage tsakanin Arsenal da Man City

April 13, 2026

Mutane sama da 50 sun rasu a kuskuren harin sojin sama a kasuwa

April 13, 2026

INEC ta ɗage aikin sabunta bayanan rajistar masu zaɓe a fadin ƙasa

April 11, 2026

Gwamnan Kano ya naɗa Bilkisu Maimota a matsayin shugabar ma’aikata ta jiha

April 11, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

By WafsymApril 2, 2026

A Jihar Kano, ana ci gaba da nuna damuwa kan yadda wasu masu anfani da…

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.