Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Hatsarin jirgin kasa daga Abuja zuwa Kaduna ya jikkata mutane da dama
Afrika

Hatsarin jirgin kasa daga Abuja zuwa Kaduna ya jikkata mutane da dama

March 17, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
1773704071560

Fasinjoji da dama sun jikkata bayan wani jirgin ƙasa da ke jigila tsakanin Abuja zuwa Kaduna ya sauka daga layin dogo sakamakon cin karo da wani abu a kan hanyarsa.

Lamarin ya faru ne yau Litinin a kusa da Asham a kan layin dogon da ke tsakanin Abuja da Kaduna, lamarin da ya jefa fasinjojin cikin fargaba.

Shugaban Hukumar Sufurin Jiragen Ƙasa (NRC), Kayode Opeifa, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa an tura tawagar agajin gaggawa nan take bayan samun rahoton hatsarin.

Binciken farko ya nuna cewa jirgin ya kauce daga hanyarsa ne bayan ya yi karo da wani abu a kan layin dogon, sai dai har yanzu jami’ai ba su fitar da cikakken bayani kan yadda lamarin ya faru ba.

Rahotanni sun ce wasu daga cikin fasinjojin da suka samu raunuka daban-daban, an garzaya da su zuwa cibiyar lafiya da ke tashar jirgin ƙasa ta Idu da ke Abuja domin samun kulawar mahukuntan lafiya.

Hukumar NRC wadda ta tabbatar da faruwar hatsarin da misalin ƙarfe 10:30 na safiyar wannan Litinin, ta ce babu wanda ya rasa ransa a hatsarin.

Wasu hotuna da ke yawo a kafafen sada zumunta sun nuna wasu daga cikin taragon jirgin da suka lalace, yayin da ma’aikatan jirgin ke duba inda abin ya faru, tare da ɗimbin fasinjojin da sun galabaita suka sauka daga jirgin suna jiran a kai su wuri mai aminci.

Hukumar NRC ta ce injin ɗaya daga cikin taragon jirgin da kuma wani tarago mai ɗaukar fasinja ne suka samu matsala sakamakon hatsarin

Opeifa ya ce an gaggauta aiwatar da matakan ceto tare da tura ƙwararrun jami’an fasaha zuwa wurin, yayin da Hukumar Tabbatar da Aminci (SIB) ke gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

Ya kuma tabbatar da cewa jirgin ya isa tashar Idu da misalin ƙarfe 10:39 na safe, inda ya samu jinkiri na mintuna 38 saboda cire sassan jirgin da hatsarin ya shafa.

Hukumar ta jaddada cewa tsaron fasinjoji shi ne babban abin da ta sa a gaba, tare da tabbatar da cewa ana ɗaukar dukkan matakan da suka dace domin tabbatar da ci gaba da gudanar da ayyukan jirgin cikin aminci.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Hukumomin yaƙi da cin hanci ba su taɓa gayyata ta ba — Pantami

April 14, 2026

An kama jami’an ƴansanda 6 tare da wasu mutane 3 bisa zargin ƙwace da satar mutane a Edo 

April 14, 2026

Maki shida ne ya rage tsakanin Arsenal da Man City

April 13, 2026

Mutane sama da 50 sun rasu a kuskuren harin sojin sama a kasuwa

April 13, 2026

INEC ta ɗage aikin sabunta bayanan rajistar masu zaɓe a fadin ƙasa

April 11, 2026

Gwamnan Kano ya naɗa Bilkisu Maimota a matsayin shugabar ma’aikata ta jiha

April 11, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

By WafsymApril 2, 2026

A Jihar Kano, ana ci gaba da nuna damuwa kan yadda wasu masu anfani da…

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.