Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Dalilin da ya sa ban ɗaga hankalina ba lokacin da na rasa muƙamai — Sanusi II
Afrika

Dalilin da ya sa ban ɗaga hankalina ba lokacin da na rasa muƙamai — Sanusi II

March 16, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
sanusi 4

Tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN) kuma Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya bayyana dalilin da ya sa bai ɗaga hankalinsa ba bayan rasa manyan muƙamai biyu a rayuwarsa.

Sanusi II, ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi a taron lakcar azumi ta shekara-shekara ta Fola Adeola (Fola Adeola Annual Ramadan Lecture).

Mun Ceto Nijeriya Yayin Da Take Gab Da Dilmiyewa – Shugaba Tinubu

A wajen taron, ya yi magana kan muhimmancin haƙuri da kuma yadda dogaro da Allah Ya taimaka masa wajen shawo kan ƙalubalen da ya fuskanta.

Ya ce mutane da dama suna kuskuren danganta nasara da iko ga ’yan adam, maimakon su gane cewa Allah ne kaɗai ke juya al’amuran yadda Ya so.

“Sau da yawa a rayuwarmu muna danganta abubuwa ga mutane, alhali su ma halittu ne kawai,” in ji Sanusi.

“Idan ka tuna cewa yanayin rayuwa ba ya dawwama, kuma Allah ne ke sauya al’amura, hakan zai taimaka maka ka jure kuma ka daidaita halayenka.”

Ya gargaɗi mutane da kada su ƙasƙantar da kansu domin neman yardar masu iko.

A cewarsa, wasu mutanen kan ƙasƙantar da kansu ne saboda tunanin cewa wani mutum ne ke da iko a kan makomarsu.

Sanusi II, ya kafa misali da rayuwarsa domin nuna yadda al’amura ke sauyawa cikin ƙanƙanin lokaci.

Ya ce: “An dakatar da ni daga muƙamin Gwamnan Babban Banki, bayan watanni uku kuma na zama Sarki. Bayan wasu shekaru aka sauke ni daga sarauta, amma bayan shekaru huɗu na sake dawowa.

“Yanzu ina cikin fada, a kan karagar mulkina… A ƙarshe dai, dogaro ga Allah ne ke yin komai. Kada ka firgita.”

Ya ƙara da cewa lokacin da yake rayuwa bayan fitar da shi daga Kano, ya ba shi damar mayar da hankali kan karatu da kuma bunƙasa ci gaban gobensa.

Sanusi II, ya riƙe muƙamin Gwamnan CBN daga shekarar 2009 zuwa 2014.

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ne, ya tsige shi daga karagar mulki a shekarar 2020.

Sai dai Gwamna Abba Kabir Yusuf ya dawo da shi kan Sarautar Kano a shekarar 2024..

 

AMINIYA

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Gwamnatin Kano Za Ta Tallafa Wa duk Wani Yunkurin Da Zai Kawar Da Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi A Jihar 

September 9, 2026

Kotu Ta Yanke Wa Mutane Biyu Daurin Shekaru 9 Kan Bai Wa Yara Kanana Kayan Shaye-shaye

September 8, 2026

Jam’iyyar Labour Party Ta Yi Alkawarin Kafa Hukumar Kula da Hayar Gidaje A Kano 

September 5, 2026

Rasuwar Ugboaja Ta Bar Babban Gibi A Ƙungiyar Ƙwadago — Abbas

August 27, 2026

Kano PHCMB Ta Nemi Haɗin Kan Al’umma Don Inganta Kiwon Lafiya

August 18, 2026

Allah Ya yi wa Alhaji Sani Gwarzo, wanda aka fi sani da “Tumbuleke”, rasuwa.

August 11, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Gwamnatin Kano Ta Yi Alƙawarin Ƙara Wa NDLEA Motoci Don Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ‎

June 29, 20267

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.