Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Jirgin sojin Amurka ya yi hatsari a Iraƙi
Babban Labari

Jirgin sojin Amurka ya yi hatsari a Iraƙi

March 13, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
f75d7270 1e66 11f1 9120 a910fc22c6ac.jpg

Wani jirgin sojin Amurka ya yi hatsari a Iraƙi, kamar yadda rundunar sojin Amurka ta tabbatar.

Jirgin sojin na KC-135 ya faɗo ne bayan wani “hatsarin” da ya shafi wasu jirage biyu.

Rundunar sojin Amurka ta ce “ana ci gaba da aikin ceto” a yammacin Iraƙi – abin da sojoji suka ce ya faru ne a “yankin da ba na maƙiya ba.”

“Lamarin ba ya faru ba ne a yankin da ake yaƙi ko kuma musayar wuta,” in ji sanarwar.

Jirgi na biyu da lamarin ya shafa ya sauka lafiya, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Babu dai tabbas kan adadin mutanen da ke cikin jirgin da kuma makomarsu.

Sannan ba a san dalilin da ya haddasa hatsarin jirgin ba, da kuma asalin wurin da hatsarin ya faru.

Ana hasashen jirgin sojin wanda ke ba jiragen yaki na Amurka mai ya yi taho mu gama ne da wani jirgin a sararin samaniya.

Irin jiragen masu tankar mai na taka rawa sosai a yaƙi, inda jiragen yaƙi da masu kai harin bama-bamai ke dogaro da su musamman idan har sai sun yi dogon zango kafin inda za su kai hari.

Rundunar sojin Amurka ta ce lamarin ya faru ne a Iraƙi amma ba a san tazarar da ke tsakanin wurin da makwabciyarta Iran ba.

Wannan na zuwa bayan rundunar sojin Faransa ta ce wani harin jirgi marar matuki ya raunata sojojinta shida a yankin Kurdawa na Iraƙi a ranar Alhamis.

An kai masu hari ne a lokacin da suke atisaye tare da dakarun Iraƙi, kamar yadda rahotanni suka nuna .

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

HARIN FARM CENTRE: Kada A Bari Rikicin Siyasa Ya Lalata Tattalin Arzikin Kano — Abbas Ibrahim

April 29, 2026

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

April 25, 2026

Sarki Sunusi ya caccaki gwamnatin tarayya kan cigaba da ciyo bashi duk da janye tallafin mai

April 24, 2026

An tabbatar da naɗin Dr Muttaqha Darma a matsayin sabon ministan gidaje

April 24, 2026

El-Rufa’i ya sake zargin yunƙurin kama shi

April 21, 2026

Dole Najeriya ta samu tsaro – Babban hafsan tsaro

April 20, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.