Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Jirgin sojin Amurka ya yi hatsari a Iraƙi
Babban Labari

Jirgin sojin Amurka ya yi hatsari a Iraƙi

March 13, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
f75d7270 1e66 11f1 9120 a910fc22c6ac.jpg

Wani jirgin sojin Amurka ya yi hatsari a Iraƙi, kamar yadda rundunar sojin Amurka ta tabbatar.

Jirgin sojin na KC-135 ya faɗo ne bayan wani “hatsarin” da ya shafi wasu jirage biyu.

Rundunar sojin Amurka ta ce “ana ci gaba da aikin ceto” a yammacin Iraƙi – abin da sojoji suka ce ya faru ne a “yankin da ba na maƙiya ba.”

“Lamarin ba ya faru ba ne a yankin da ake yaƙi ko kuma musayar wuta,” in ji sanarwar.

Jirgi na biyu da lamarin ya shafa ya sauka lafiya, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Babu dai tabbas kan adadin mutanen da ke cikin jirgin da kuma makomarsu.

Sannan ba a san dalilin da ya haddasa hatsarin jirgin ba, da kuma asalin wurin da hatsarin ya faru.

Ana hasashen jirgin sojin wanda ke ba jiragen yaki na Amurka mai ya yi taho mu gama ne da wani jirgin a sararin samaniya.

Irin jiragen masu tankar mai na taka rawa sosai a yaƙi, inda jiragen yaƙi da masu kai harin bama-bamai ke dogaro da su musamman idan har sai sun yi dogon zango kafin inda za su kai hari.

Rundunar sojin Amurka ta ce lamarin ya faru ne a Iraƙi amma ba a san tazarar da ke tsakanin wurin da makwabciyarta Iran ba.

Wannan na zuwa bayan rundunar sojin Faransa ta ce wani harin jirgi marar matuki ya raunata sojojinta shida a yankin Kurdawa na Iraƙi a ranar Alhamis.

An kai masu hari ne a lokacin da suke atisaye tare da dakarun Iraƙi, kamar yadda rahotanni suka nuna .

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Hukumomin yaƙi da cin hanci ba su taɓa gayyata ta ba — Pantami

April 14, 2026

An kama jami’an ƴansanda 6 tare da wasu mutane 3 bisa zargin ƙwace da satar mutane a Edo 

April 14, 2026

Maki shida ne ya rage tsakanin Arsenal da Man City

April 13, 2026

Mutane sama da 50 sun rasu a kuskuren harin sojin sama a kasuwa

April 13, 2026

INEC ta ɗage aikin sabunta bayanan rajistar masu zaɓe a fadin ƙasa

April 11, 2026

Gwamnan Kano ya naɗa Bilkisu Maimota a matsayin shugabar ma’aikata ta jiha

April 11, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

By WafsymApril 2, 2026

A Jihar Kano, ana ci gaba da nuna damuwa kan yadda wasu masu anfani da…

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.