Daga wannan Lahadi farashin man fetur a birnin Legas na Najeriya ya yi tashin gwauron zabi, inda yanzu ya kai tsakanin ₦1,040 zuwa ₦1,080 a kowace lita a gidajen mai daban-daban.
Wannan ƙarin ya biyo bayan hauhawar farashin ɗanyen mai a kasuwar duniya, sakamakon faɗaɗa yaƙi tsakanin kasashen Amurka, Isra’ila, da kuma Iran wanda ke barazana ga harkar man fetur.
Tashin hankali a yankin Gabas Ta Tsakiya, wanda ya haɗa da hare-hare kan jagororin Iran da cibiyoyin man fetur, ya sanya farashin ɗanyen mai na Brent ya kusanci dala $90 zuwa $100 a kowace ganga.
Wannan lamari ya jefa kasuwannin duniya cikin ɗar-ɗar, wanda ke shafar kasashe masu shigo da tataccen mai kamar Najeriya kai-tsaye.
A nan gida, matatun mai sun fara daidaita farashinsu don dacewa da halin da ake ciki, inda matatar man Dangote ta kara farashi daga ₦874 zuwa ₦995 a cikin kwanaki huɗu kacal.
Kamfanin ya bayyana cewa tsadar danyen mai da ake sayowa don tacewa ita ce babban dalilin da ya tilasta wannan karin farashin.
Gidajen man na kamfanin NNPC Retail da ke sassan Legas su ma sun sauya farashinsu zuwa kusan ₦1,040 a kowace lita, daga tsohon farashin da yake kusan ₦993.
Sauran gidajen mai masu zaman kansu irinsu Techno Oil, Mobil, da MRS su ma suna sayar da man a kan farashi daban-daban da ya kama daga ₦1,050 har zuwa kusan ₦1,100 a wasu wuraren.
Masana tattalin arziki sun yi gargadin cewa idan har rikicin Iran ya kai ga toshe mashigin ruwa na Hormuz, farashin ɗanyen mai na iya haura dala $120 zuwa $130 akan kowace ganga.
Idan hakan ta faru, akwai yiwuwar farashin fetur a Najeriya ya kai ₦1,200 ko fiye da haka, wanda zai kara tsananta halin rayuwa ga talaka.
Wannan hauhawar farashin man tuni ya fara shafar farashin abinci da sufuri a fadin kasar, yayin da direbobin motocin haya ke korafin tsadar man. Jama’a na ci gaba da sanya ido kan yadda diflomasiyyar duniya za ta karkata don ganin ko za a samu saukin wannan rikici da ya addabi tattalin arzikin duniya.

