Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Yakin Amurka/Isra’ila da Iran: Lallai da ni za a zaɓi sabon shugaba a Iran – Trump
Babban Labari

Yakin Amurka/Isra’ila da Iran: Lallai da ni za a zaɓi sabon shugaba a Iran – Trump

March 6, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
709995 750x375

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana cewa yana bukatar a saka Amurka cikin tsarin zaben sabon shugaban Iran.

Trump ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da kafar yada labarai ta Axios ranar Alhamis, kwanaki biyar bayan kashe jagoran addinin Iran, Ayatollah Ali Khamenei, a wani hari da Amurka da Isra’ila suka kai kan gidansa a Tehran.

Majalisar Dokokin Kano ta fara yunƙurin tsige mataimakin Gwamna

A cewar Trump, Iran na bata lokacinta idan ta yi kokarin nada sabon jagora ba tare da sa hannun Amurka ba.

Ya kuma bayyana cewa Mojtaba Khamenei, ɗan marigayi Ali Khamenei wanda ake ganin zai iya gaje shi, ba zabin da zai amince da shi ba.

Trump ya bayyana shi a matsayin mutum mara karfi, yana mai cewa:

“Dan Khamenei ba zabin da zan amince da shi ba. Muna son wanda zai kawo zaman lafiya da hadin kai a Iran.”

Ya kara da cewa dole ne shi kansa ya shiga cikin tsarin zaben sabon shugaban, yana mai kwatanta lamarin da yadda Amurka ta shiga cikin sauyin shugabanci a Venezuela.

Trump ya kuma ce ba zai amince da duk wani sabon shugaban Iran da zai ci gaba da manufofin gwamnatin da ta gabata ba.

A cewarsa, idan hakan ta faru, za a iya sake samun rikici tsakanin Amurka da Iran cikin shekaru biyar masu zuwa.

Tun da farko, Trump ya ce mafi munin sakamakon yakin da ake yi yanzu shi ne idan wani shugaba mai tsattsauran ra’ayi kamar marigayi Khamenei ya karbi mulki.

Ya kuma bayyana cewa wasu daga cikin mutanen da Amurka ta yi tunanin za su iya jagorantar Iran sun mutu a hare-haren farko da aka kai.

Kalaman Trump na zuwa ne yayin da yakin da Amurka da Isra’ila suka kaddamar kan Iran ke ci gaba, inda rahotanni suka nuna cewa sama da Iraniyawa 1,000 sun mutu, yayin da sojojin Amurka shida da mutane 11 a Isra’ila suka rasa rayukansu sakamakon hare-haren Iran.zaɓi sabon shugaba a Iran – Trump.

 

Premium times

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Sojojin UAE biyu sun mutu a hatsarin jirgin sama – Ma’aikatar tsaro

March 10, 2026

Mojtaba Khamenei Ya Gaji Mahaifinsa A Matsayin Jagoran Addinin Iran

March 9, 2026

Farashin litar man fetur ya zarce naira dubu 1 a sassan Najeriya

March 9, 2026

Mutanen da ake hasashen za su maye gurbin Mataimakin Gwamnan Kano

March 7, 2026

Majalisar Dokokin Kano ta fara yunƙurin tsige mataimakin Gwamna

March 6, 2026

Gwamnatin Jigawa Ta Tsige Alƙalin Kotun Musulunci Kan Rashawa

March 4, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Bincike Na Musamman

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

By WafsymMarch 9, 2026

‎Rundunar Kano Neighbourhood Watch Security Corps, wadda gwamnatin Jihar Kano ta kafa domin tallafawa hukumomin…

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026

KANO: Farashin Kayan Masarufi Ya Yi Tashin Gwauron Zabi Gabanin Shigowar Azumin Ramadan ‎ ‎

February 12, 2026

‎“Ya Kamata ‘Yan Jaridu Su Riƙa Nuna Tausayi, Hikima Da Mutunta Jinƙan Ɗan Adam wajen ɗauko labarai ‎ ‎ ‎—Comrade Abbas Ibrahim

January 21, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.