Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Jami’an ’Yan Sanda Sun Dakatar Da Wasan Tashe A Kano
Afrika

Jami’an ’Yan Sanda Sun Dakatar Da Wasan Tashe A Kano

March 1, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
images42

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta sanar da dakatar da wasan gargajiya na Tashe a duk faɗin jihar a wannan watan na Ramadan, saboda dalilan tsaro.

Hukumar ta ce an ɗauki matakin ne tare da haɗin gwiwar gwamnatin jihar domin hana masu aikata laifi amfani da tarukan Tashe wajen aikata miyagun ayyuka, ciki har da daba, ƙwacen waya da kuma shaye-shayen miyagun ƙwayoyi.

Tinubu ya sake naɗa Abubakar Audi a Kwamanda Janar Na NSCDC

Kwamishinan ’yan sandan jihar, Ibrahim Adamu Bakori, ya bayyana cewa rundunar ta tanadi matakan tsaro domin tabbatar da an gudanar da azumin cikin zaman lafiya da kwanciyar hankali. Ya kuma buƙaci iyaye da masu kula da yara su ƙara sa ido, tare da gargadin matasa kan shiga duk wani taro da ka iya haddasa tashin hankali ko karya doka.

A cewarsa, duk wanda aka samu da laifin karya doka zai fuskanci hukunci mai tsanani.

A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Abdullahi Haruna Kiyawa, ya fitar, ya buƙaci jama’a su riƙa kai rahoton duk wani motsi da ba su yarda da shi ba ta lambobin waya:

08032419754, 08123821575, 08076091271, 09029292926,

ko kuma ta manhajar NPF Rescue Me da ake samu a Play Store.

Rundunar ta jaddada cewa haɗin kan al’umma da hukumomin tsaro na da muhimmanci wajen tabbatar da zaman lafiya a duk tsawon watan Ramadan.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Gwamna Abba Ya Kaddamar da Kwamitin Yaƙi da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi, Ya Sanya Hannu Kan Dokar Daba A Kano

July 22, 2026

Sakamakon Binciken Jami’ar Northwest Kano Ya Haskaka Matsalolin Lafiyar Al’umma a Tofa

July 14, 2026

“Rikicin Shaidar Zama Ɗan Ƙasa a Jos North Ya Ɗauki Sabon Salo, Sarakunan Gargajiya Sun Nemi Shiga Cikin Shari’a.”

July 11, 2026

Sarkin Gaya: Mallakar Katin Zaɓe Shi Ne Ginshiƙin Zaɓen Shugabanni Nagari

July 3, 2026

Sahihin ‎Labari Ke Tabbatar Da Amincewar Jama’a, Ba Gaggawar Wallafa Ba- Shugaban NUJ

July 1, 2026

NWUK Expels 34 Students Over Examination Malpractice

June 30, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Gwamnatin Kano Ta Yi Alƙawarin Ƙara Wa NDLEA Motoci Don Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ‎

June 29, 20267

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.