Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Jami’an ’Yan Sanda Sun Dakatar Da Wasan Tashe A Kano
Afrika

Jami’an ’Yan Sanda Sun Dakatar Da Wasan Tashe A Kano

March 1, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
images42

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta sanar da dakatar da wasan gargajiya na Tashe a duk faɗin jihar a wannan watan na Ramadan, saboda dalilan tsaro.

Hukumar ta ce an ɗauki matakin ne tare da haɗin gwiwar gwamnatin jihar domin hana masu aikata laifi amfani da tarukan Tashe wajen aikata miyagun ayyuka, ciki har da daba, ƙwacen waya da kuma shaye-shayen miyagun ƙwayoyi.

Tinubu ya sake naɗa Abubakar Audi a Kwamanda Janar Na NSCDC

Kwamishinan ’yan sandan jihar, Ibrahim Adamu Bakori, ya bayyana cewa rundunar ta tanadi matakan tsaro domin tabbatar da an gudanar da azumin cikin zaman lafiya da kwanciyar hankali. Ya kuma buƙaci iyaye da masu kula da yara su ƙara sa ido, tare da gargadin matasa kan shiga duk wani taro da ka iya haddasa tashin hankali ko karya doka.

A cewarsa, duk wanda aka samu da laifin karya doka zai fuskanci hukunci mai tsanani.

A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Abdullahi Haruna Kiyawa, ya fitar, ya buƙaci jama’a su riƙa kai rahoton duk wani motsi da ba su yarda da shi ba ta lambobin waya:

08032419754, 08123821575, 08076091271, 09029292926,

ko kuma ta manhajar NPF Rescue Me da ake samu a Play Store.

Rundunar ta jaddada cewa haɗin kan al’umma da hukumomin tsaro na da muhimmanci wajen tabbatar da zaman lafiya a duk tsawon watan Ramadan.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

HARIN FARM CENTRE: Kada A Bari Rikicin Siyasa Ya Lalata Tattalin Arzikin Kano — Abbas Ibrahim

April 29, 2026

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

April 25, 2026

Sarki Sunusi ya caccaki gwamnatin tarayya kan cigaba da ciyo bashi duk da janye tallafin mai

April 24, 2026

An tabbatar da naɗin Dr Muttaqha Darma a matsayin sabon ministan gidaje

April 24, 2026

Majalisa ta buƙaci a dakatar da yaƙin neman zaɓe a jihohin arewa 8 saboda matsalar tsaro

April 24, 2026

Hon.Sha’aban ya jaddada janye neman takarar Sanatan Kaduna ta Arewa, tare da bayyana goyon duk wanda APC ta tsayar 

April 21, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.