Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Manyan Labarai INEC ta sauya jadawalin Zaɓen 2027
Afrika

Manyan Labarai INEC ta sauya jadawalin Zaɓen 2027

February 27, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
inec

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ayyana Asabar, 16 ga Janairun 2027, a matsayin ranar gudanar da Zaɓen Shugaban Ƙasa da Majalisar Tarayya.

Kwamishinan hukumar na ƙasa kuma Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Masu Kaɗa Ƙuri’a, Mohammed Haruna, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis a Abuja.

Ya ƙara da cewa, za a gudanar da zaɓen gwamnoni da na majalisun jihohi a ranar Asabar, 6 ga Fabrairu, 2027.

INEC ta ce ta fara tattaunawa da masu ruwa da tsaki domin samun maita ga ƙorafin da wasu ke yi game da jaddawalin zaɓen 2027 da ta fitar, wanda ya nuna za a yi zaɓen a cikin azumi.

A makonnin bayan nan ne INEC ta bai wa ’yan Najeriya tabbacin cewa a tsaye take domin ganin ta yi la’akari da buƙatun kowanne ɓangare na al’umma wajen tsara ayyukan ta.

A farkon watan nan ne hukumar zaɓen ta sanar da cewa za ta gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na ’yan majalisar dokokin tarayya a ranar 20 ga watan Fabarairun 2027, yayin da na gwamnoni da ’yan majalisar dokokin jihohi zai gudana a ranar 6 ga watan Faburairun 2027.

Sai dai sanarwar hukumar zaɓen ta bar baya da ƙura, inda wasu ’yan Najeriya musamman musulmai suka bayyana damuwa kan yadda jadawalin na INEC ke nuna cewa zaɓen zai gudana ne a lokacin azumin watan Ramadana na baɗi.

Masu wannan damuwa na ganin cewa hakan zai shafi musulmai ta la’akari da yadda wasu za su gaza jure fita kaɗa ƙuri’a cikin yanayi na azumi, da kuma yadda yanayin zai iya shafar ƙwazon ma’aikatan INEC da za su kasance cikin azumin lokacin.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Sojojin UAE biyu sun mutu a hatsarin jirgin sama – Ma’aikatar tsaro

March 10, 2026

Mojtaba Khamenei Ya Gaji Mahaifinsa A Matsayin Jagoran Addinin Iran

March 9, 2026

Farashin litar man fetur ya zarce naira dubu 1 a sassan Najeriya

March 9, 2026

Mutanen da ake hasashen za su maye gurbin Mataimakin Gwamnan Kano

March 7, 2026

Yakin Amurka/Isra’ila da Iran: Lallai da ni za a zaɓi sabon shugaba a Iran – Trump

March 6, 2026

Majalisar Dokokin Kano ta fara yunƙurin tsige mataimakin Gwamna

March 6, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Bincike Na Musamman

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

By WafsymMarch 9, 2026

‎Rundunar Kano Neighbourhood Watch Security Corps, wadda gwamnatin Jihar Kano ta kafa domin tallafawa hukumomin…

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026

KANO: Farashin Kayan Masarufi Ya Yi Tashin Gwauron Zabi Gabanin Shigowar Azumin Ramadan ‎ ‎

February 12, 2026

‎“Ya Kamata ‘Yan Jaridu Su Riƙa Nuna Tausayi, Hikima Da Mutunta Jinƙan Ɗan Adam wajen ɗauko labarai ‎ ‎ ‎—Comrade Abbas Ibrahim

January 21, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.