Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Ƙalubalen da ke gaban sabon Sufeto Janar na ‘yansandan Nijeriya
Afrika

Ƙalubalen da ke gaban sabon Sufeto Janar na ‘yansandan Nijeriya

February 26, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
Tunji Disu1

Tun bayan naɗin sabon Sufeto Janar na ’yan sanda a Nijeriya wasu masana tsaro suka fara sharhi kan dimbin kalubalen da ke gabansa, musamman idan aka yi la’akari da tarin matsalolin tsaron da kasar take fama da su a halin yanzu.

Olatunji Rilwan Disu ya maye gurbin Kayode Egbetokun ne wanda ya yi murabus ranar Talata. A watan Yunin 2023 ne Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya naɗa Kayode Egbetokun a matsayin Sufeto Janar na ‘yansandan

An haifi sabon mukaddashin ’yan sandan ne a jihar Legas da ke kudu masu yammacin Nijeriya ranar 13 ga watan Afrilun 1966.

Ya shiga aikin ɗansanda ne a ranar 18 ga watan Mayun 1992, inda ake sa ran zai yi ritaya daga aiki a cikin wannan shekara saboda zai cika shekara 60 cif a duniya a cikin watan Afrilu mai zuwa. Ko da yake saboda gyarar da majalisar dokokin kasar ta yi wa dokar ’yansanda wato Police Act a watan Yulin shekarar 2024, yanzu sabon sufeto janar din zai iya kammala wa’adinsa na shekaru hudu, sai dai idan bisa radin kansa ya zabi ya yi murabus ko kuma shugaban kasa ya sauke shi daga kujerar.

Tunji Disu shi ne ya shugabanci sashen kai ɗauki da tattara bayanan sirri na rundunar ƴansandan kasar bayan sauke wanda ya gabace shi, Abba Kyari a shekarar 2021.

Babban kalubalen da sabon sufeto janar din ’yan sanda zai yi fama da shi ne batun tsaro wanda ya hada da matsalar satar mutane don neman kudin fansa da hare-haren ’yanfashin daji da matsalar Boko Haram da ISWAP da ta Lakurawa da rikicin makiyaya da manoma da sauransu.

A makonni uku na wannan wata an kashe fiye da mutum 330 a arewacin Nijeriya. Masana harkokin tsaro suna yawan cewa yana da wuya ka samu kasa wacce ba ta cikin yaki da za a rika kashe mutane barkatai haka.

Shugaban kamfanin tsaro na Beacon Consulting a Nijeriya kuma masanin kan al’amuran da suka shafi tsaro Dokta Kabiru Adamu ya taba shaida wa TRT Afrika Hausa cewa mutum fiye da 10,000 suka mutu a Nijeriya a shekarar 2025 sanadin matsalolin tsaron da kasar take fama da su.

Sannan wani kalubale da ke gaban sabon Sufeto Janar din ’yansandan shi ne inganta yanayin aikin ’yansanda ta hanyar bunkasa albashi da walwalarsu da kuma samar musu kayan aiki na zamani da suke bukata.

Inganta tsarin albashin ’yansanda yana da muhimmanci sosai saboda kamar yadda wasu masana suke fada, hakan zai taimaka wajen rage matsalar karbar cin hanci da rashawa ake yawan zarginsu da yi.

Kazalika wani abu da ya kamata sabon Sufeto Janar din ya ba muhimmanci shi ne batun tattara bayanan sirri da amfani da su wajen dakile barazanar tsaro kafin matala ta auku, kamar yadda masana tsaro suke yawan bayar da shawara.

Sannan batun daukar sabbin kananan ’yansanda 50,000 da Shugaba Bola Tinubu ya yi alkawari a watan Nuwamban bara lokacin da ya ayyana dokar ta-baci kan harkar tsaro a kasar, masana na ganin hanzarta yin hakan zai taimaka sosai wajen tunkarar matsalolin tsaron da kasar take fama da su a yanzu.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Gwamnan Kano ya sauke shugaban ma’aikatan jihar Alhaji Abdullahi Musa daga mukaminsa

March 11, 2026

Sojojin UAE biyu sun mutu a hatsarin jirgin sama – Ma’aikatar tsaro

March 10, 2026

Mojtaba Khamenei Ya Gaji Mahaifinsa A Matsayin Jagoran Addinin Iran

March 9, 2026

Farashin litar man fetur ya zarce naira dubu 1 a sassan Najeriya

March 9, 2026

Mutanen da ake hasashen za su maye gurbin Mataimakin Gwamnan Kano

March 7, 2026

Yakin Amurka/Isra’ila da Iran: Lallai da ni za a zaɓi sabon shugaba a Iran – Trump

March 6, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Bincike Na Musamman

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

By WafsymMarch 11, 2026

Sabbin matakan da Majalisar Dokokin Jihar Kano ta dauka na fara shirin tsige Mataimakin Gwamna,…

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026

KANO: Farashin Kayan Masarufi Ya Yi Tashin Gwauron Zabi Gabanin Shigowar Azumin Ramadan ‎ ‎

February 12, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.