Wasu ’yan majalisar dokokin Amurka ƙarƙashin jagorancin ɗan majalisa Riley Moore, sun miƙa wa Fadar White House wani rahoto na musamman kan zargin tsananta wa Kiristoci a Najeriya, inda suka jaddada buƙatar a sanyawa ƙasar takunkumi.
Rahoton ya ba da shawarar sanyawa da kuma jaddada takunkumin hana biza ga duk mutumin da aka samu da hannu wajen tauye hakkin addini ko kisan Kiristoci a Najeriya.
Dakarun Soji Sun Daƙile Harin Lakurawa Kan Wata Kasuwa a Kebbi
Wannan rahoto ya biyo bayan bincike ne da Shugaba Trump ya umarci Riley Moore da Tom Cole su jagoranta, inda suka bayyana Najeriya a matsayin kasa mafi hadari a duniya ga Kiristoci.
‘Yan majalisar sun buƙaci gwamnatin Amurka ta yi nazarin dakatar da shigo da naman shanu da sauran kayayyaki daga Najeriya don matsa lamba ga makiyaya masu ɗauke da makami su ajiye makamansu.
Rahoton ya goyi bayan matakin Shugaba Donald Trump na sake sanya Najeriya a cikin jerin ƙasashen da ke da matsalar ƙuntatawa kirstoci.
‘Yan majalisar sun buƙaci Najeriya ta soke dokokin shari’a da na ɓatanci waɗanda suka ce ana amfani da su wajen gallaza wa Kiristoci.
Sun kuma ba da shawarar dakatar da wasu tallafin kudi da Amurka ke ba wa Najeriya har sai gwamnatin ƙasar ta ɗauki matakan zahiri na dakatar da tashe-tashen hankula.
Tawagar ta Riley Moore ta kuma bayar da shawarar cewa Najeriya ta daina sayen makaman Rasha, maimakon haka ta sayi na Amurka a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar tsaro ta haɗin gwiwa.
Gwamnatin Najeriya dai ta sha musanta waɗannan zarge-zarge, tana mai cewa rikice-rikicen da ke faruwa a ƙasar basu da alaƙa da addini, illa ‘yan ta’adda da ke addabar mabiya mabanbantan addinai.

