Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Amurka Ta Buƙaci Najeriya Ta Katse Cinikin makamai da Rasha
Afrika

Amurka Ta Buƙaci Najeriya Ta Katse Cinikin makamai da Rasha

February 25, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
tinubu and trump 750x536 1

Wasu ’yan majalisar dokokin Amurka ƙarƙashin jagorancin ɗan majalisa Riley Moore, sun miƙa wa Fadar White House wani rahoto na musamman kan zargin tsananta wa Kiristoci a Najeriya, inda suka jaddada buƙatar a sanyawa ƙasar takunkumi.

Rahoton ya ba da shawarar sanyawa da kuma jaddada takunkumin hana biza ga duk mutumin da aka samu da hannu wajen tauye hakkin addini ko kisan Kiristoci a Najeriya.

Dakarun Soji Sun Daƙile Harin Lakurawa Kan Wata Kasuwa a Kebbi

Wannan rahoto ya biyo bayan bincike ne da Shugaba Trump ya umarci Riley Moore da Tom Cole su jagoranta, inda suka bayyana Najeriya a matsayin kasa mafi hadari a duniya ga Kiristoci.

‘Yan majalisar sun buƙaci gwamnatin Amurka ta yi nazarin dakatar da shigo da naman shanu da sauran kayayyaki daga Najeriya don matsa lamba ga makiyaya masu ɗauke da makami su ajiye makamansu.

Rahoton ya goyi bayan matakin Shugaba Donald Trump na sake sanya Najeriya a cikin jerin ƙasashen da ke da matsalar ƙuntatawa kirstoci.

‘Yan majalisar sun buƙaci Najeriya ta soke dokokin shari’a da na ɓatanci waɗanda suka ce ana amfani da su wajen gallaza wa Kiristoci.

Sun kuma ba da shawarar dakatar da wasu tallafin kudi da Amurka ke ba wa Najeriya har sai gwamnatin ƙasar ta ɗauki matakan zahiri na dakatar da tashe-tashen hankula.

Tawagar ta Riley Moore ta kuma bayar da shawarar cewa Najeriya ta daina sayen makaman Rasha, maimakon haka ta sayi na Amurka a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar tsaro ta haɗin gwiwa.

Gwamnatin Najeriya dai ta sha musanta waɗannan zarge-zarge, tana mai cewa rikice-rikicen da ke faruwa a ƙasar basu da alaƙa da addini, illa ‘yan ta’adda da ke addabar mabiya mabanbantan addinai.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Gwamnan Kano ya sauke shugaban ma’aikatan jihar Alhaji Abdullahi Musa daga mukaminsa

March 11, 2026

Sojojin UAE biyu sun mutu a hatsarin jirgin sama – Ma’aikatar tsaro

March 10, 2026

Mojtaba Khamenei Ya Gaji Mahaifinsa A Matsayin Jagoran Addinin Iran

March 9, 2026

Farashin litar man fetur ya zarce naira dubu 1 a sassan Najeriya

March 9, 2026

Mutanen da ake hasashen za su maye gurbin Mataimakin Gwamnan Kano

March 7, 2026

Yakin Amurka/Isra’ila da Iran: Lallai da ni za a zaɓi sabon shugaba a Iran – Trump

March 6, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Bincike Na Musamman

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

By WafsymMarch 11, 2026

Sabbin matakan da Majalisar Dokokin Jihar Kano ta dauka na fara shirin tsige Mataimakin Gwamna,…

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026

KANO: Farashin Kayan Masarufi Ya Yi Tashin Gwauron Zabi Gabanin Shigowar Azumin Ramadan ‎ ‎

February 12, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.