A wani yanayi da matsalolin tsaro ke ci gaba da ta’azzara a jihohin yankin arewa maso yammacin Najeriya, ƴanbindiga sun buƙaci malamai su biya harajin naira miliyan 100 gabanin samun damar yin wa’azi a wani yanki na jihar Kebbi.
Al’umma sun shiga tashin hankali a garin Utouno na ƙaramar hukumar Ngaski da ke jihar ta Kebbi guda cikin jihohin da ke fama da matsalar tsaron, bayan samun umarnin biyan wannan kuɗi gabanin gudanar da wa’azi ko kuma Tafsiri cikin watan da muke na azumin Ramadana.
Shugaba Tinubu ya taya murna ga waɗanda suka lashe zaɓukan Abuja, Kano da Rivers
Wasu majiyoyi sun ce ƴan ta’addan sun aika ta wasiƙa da shugabannin gargajiya na yanki har ma da malumman da ke gudanar da wa’azin inda suka nemi su biya tsabar kuɗin har naira miliyan 100 gabanin samun damar yin wa’azin.
Wasiƙar ƴanbindigan ta yi gargaɗin fuskantar hukunci ga duk waɗanda suka bijirewa biyan harajin yin wa’azin.
Wannan umarni na ƴanbindigar na zuwa ne a wani yanayi da ake ganin ta’azzarar hare-haren ƴan ta’addan da ake kira Lakurawa waɗanda suka kai hari ƙaramar hukumar Kangiwa tare da kashe mutane 33.
Mazaunin wani gari da suka samu wannan wasiƙa daga ƴanbindigar wanda kuma ya nemi a sakaya sunanshi ya ce hankalin jama’a ya tashi matuƙa a yankinsu, wanda ya sanya hatta malamai shiga fargabar iya gudanar da wa’azin.
Tuni dai Gwamnan jihar Nasir Idris ya yi umarnin aikewa da ƙarin dakaru zuwa yankin don bayar da cikakkiyar kariya ga jama’a.
Bisa al’ada watan Ramadana lokaci ne da akan gudanar da karatuttukan tare da mabanbatan wa’azi iri iri don sake kusanta jama’a da mahaliccinsu.

