Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta Najeriya ICPC ta sanar cewa tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasiru El-Rufai, na hannunta daga jiya ranar Laraba 18 ga Fabrairu 2026.
Sanarwar wadda mai magana da yawun hukumar, J. Okor Odey, ya fitar ta ce “El-Rufai na hannun mu a halin yanzu domin tambayoyi masu alaƙa da bincike, kuma yana cikin kulawar hukumar a halin yanzu.”
Da Dumi Dumi An ga watan Azumi a Nijeriya
Hakan na zuwa ne bayan da tsohon gwamnan ya shafe kwanaki biyu a hannun EFCC, inda ya kai kansa ranar Litinin domin amsa gayyata kafin daga bisani aka miƙa shi ga ICPC domin ci gaba da bincike.
Har yanzu babu cikakken bayani daga hukumomin kan takamaiman zarge-zargen da ake bincikensa a kai, amma masu lura da al’amuran siyasa na cewa lamarin na ƙara jawo hankali duba da matsayin El-Rufai a siyasar ƙasar.
El-Rufai dai wanda ke cikin jagororin adawa a ADC da ke shirin ƙalubalantar shugaban ƙasa Bola Tinubu na APC a zaɓe mai zuwa, ya zargi gwamnati da matsa wa ‘yan adawa lamba ta hanyar binciken rashawa.

