Wata tirela ta murkushe mutum biyu har lahira a kan babban titin Nnamdi Azikiwe da ke cikin garin Kaduna a daren Talata.
Shaidun gani da ido sun ce mutanen da abin ya rutsa da su, namiji da mace, suna kan babur ne lokacin da tirelar ta kwace ta taka su, inda suka mutu nan take wajen misalin karfe 9:00 na dare.
Shugaba Tinubu Ya Naɗa Ambasada Ismail Abba Yusuf A Matsayin Shugaban NAHCON
Wani shaidan da ya zanta da Wakila Jaridar AMINIYA ya ce lamarin ya tayar masa da hankali, inda ya ce, “Gaskiya abin babu dadi. Namijin da macen suna kan babur, kuma babu wanda ya san daga inda suka fito. Nan take duka su biyu suka mutu.”
Daga bisani jami’an ’yan sanda sun isa wurin tare da dauke gawarwakin zuwa asibiti.
Kwamandan Hukumar Kiyaye Hadura ta Kasa (FRSC) na shiyyar Kaduna, Tijjani Iliyasu, ya tabbatar wa Aminiya faruwar lamarin.
Ya ce sun samu rahoton wata tirela ta taka mutum biyu a kan hanyar, inda ya kara da cewa ana aikin gyaran hanya a wurin, wanda hakan ke bukatar direbobi su yi hakuri tare da tuki cikin natsuwa da kulawa.
“Ana aikin gyaran hanyar, don haka ya zama dole direbobi su yi hakuri su kuma guji tukin ganganci. Abin takaici, da yawa daga cikinsu ba sa hakuri, kuma wannan ce matsalar,” in ji shi.
Ya kuma yi kira ga masu ababen hawa da su rika bin dokokin hanya tare da yin tuki cikin hakuri da natsuwa domin rage yawaitar haduran da ake samu a hanyoyin kasar nan.

