Tsohon shugaban hukumar Alhazan Najeriya, Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan ya bayyana dalilansa na ajiye aiki.
Cikin sanarwarsa ta ajiye aiki da aka wallafa a shafin NAHCON, Farfesa Pakistan ya ce ya ajiye aikin en bisa dalilansa na raɗin kai.
A ranar Litinin da maraice ne bayanai suka fara fitowa game da ajiye aikin Pakistan.
Jihar Abia Ta Sanya Hannu Kan Dokar Tallafin Tsofaffi
Cikin wasiƙar ajiye aikin nasa, Farfesa Pakista ya ce ya aike wa Shugaba Tinubu wasiƙa tare da sanar da shi matakin da ya ɗauka na ajiye aiki.
Farfesa ya gode wa shugaban ƙasar bisa ”alfarmar” da ya ce ya ba shi na jan ramagar hukumar, alfarmar da ya ce ba zai manta da ita ba har abada.
Pakistan ya ce ya ɗauki matakin ne bayan tuntuɓar ƴa’uwa da abokan arzikinsa.
A watan Oktoban 2025 ne dai wasu jami’ai a hukumar alhazan suka yi zargin yawaitar cin hanci da rashawa a ayyukan hukumar, zargin da hukumar ta sha musantawa.
A watan Agustan 2024 ne dai Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya naɗa Abdullahi Pakistan a matsayin sabon shugaban NAHCON, bayan sauke tsohon shugaban hukumar Jalal Arabi.

