Akalla jami’an rundunar ’yansandan Nijeriya 5,000 ake sa ran za su yi ritaya a shekarar 2026, in ji Mataimakin Kwamishinan ’Yansanda mai kula da fansho a shalƙwatar NPF, DCP Sani Doki Yusuf.
Yusuf ya bayyana hakan ne a Kano yayin taron horaswa na yankin Arewa maso Yamma ga jami’an da ke shirin ritaya, wanda NPF Pensions Limited ta shirya. Ya ce taron na da nufin wayar da kai kan muhimmancin cika takardun fansho yadda ya kamata domin kauce wa jinkiri wajen biyan haƙƙoƙi.
Jami’an Ƴansanda 5,000 Ake Sa Ran Za Su Yi Ritaya A Shekarar 2026
Ya ce matsalolin da ake fuskanta a biyan fansho sun fi shafar kurakurai a bayanan sirri, musamman bambancin suna da rashin daidaiton takardu, inda hukumar ke kai ziyara rundunoni domin gyara irin waɗannan matsaloli.
A cewarsa, NPF Pensions ta biya jimillar Naira biliyan 97.5 ga tsofaffin jami’ai 30,370 tun bayan kafuwarta, tare da biyan Naira biliyan 39.57 ga ’yan uwan jami’an da suka rasu 8,847. Haka kuma, tsofaffin jami’ai 25,572 na karɓar fansho na wata-wata sama da Naira biliyan 1.56.
Haka zalika, Darakta a Hukumar Fanshon ’Yansanda kuma Jami’ar Inshora ta Rundunar, ACP Lydia Ameh, ta ce jinkirin biyan fansho ya ragu matuƙa, inda ta jaddada cewa jami’an da suka cika takardunsu yadda ya dace na iya karɓar haƙƙinsu cikin kwanaki uku zuwa biyar na aiki.

