Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Shalkwatar tsaron Najeriya ta tabbatar da yunƙurin juyin mulki a watan Oktoban bara
Babban Labari

Shalkwatar tsaron Najeriya ta tabbatar da yunƙurin juyin mulki a watan Oktoban bara

January 27, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
President Bola Ahmed Tinubu
President Bola Ahmed Tinubu

Shalkwatar tsaron Najeriya ta tabbatar da fuskantar yunƙurin juyin mulki ga gwamnatin ƙasar a kwanakin baya, wanda ta ce ta gano hakan ne bayan tsananta bincike kan wasu jami’anta da ta zarga da rashin ɗa’a inda sakamako ya tabbatar da cewa tabbas sun yi shirin kifar da gwamnatin ƙasar.

Tun a watan Oktoban 2025 ne, shalkwatar tsaron Najeriyar ta sanar da kame wasu manyan sojoji 16 bayan zarginsu da saɓa dokokin aiki, kodayake a wancan lokaci ta ƙi amsa zargin cewa sun yi shirin kifar da gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu ne.

Ƙungiyar ‎SERAP Ta Maka Ministan Wutar Lantarki Da NBET Kotu Kan Zargin Badakalar N128bn  ‎‎

A wancan lokaci wata kafar labarai a Najeriyar ta ruwaito cewa sashen tattara bayanan sirri na Najeriyar ya kame Sojojin masu muƙamai daga kyaftin zuwa Birgediya Janar su 16 lokacin da suke gudanar da wani taron sirri kan shirin kifar da gwamnati.

Kafar a wancan lokaci ta alaƙanta matakin soke faretin ranar 1 ga watan Oktoba da yunƙurin juyin mulkin, sai dai a wancan lokaci daraktan yaɗa labarai na shalkwatar Birgediya Tukur Gusau ya yi watsi da zargin wanda ya ce yunƙuri ne na haddasa yamutsi a tsakanin jama’ar ƙasar.

Sai dai da ya ke ƙarin haske kan lamarin a wannan Litinin, Manjo Janar Sama’ila Uba ya ce bayan dogon bincike irin na Soji kan Jami’an, ya tabbata suna kitsa shirin kifar da gwamnatin ta Najeriya.

A cewar Manjo Sama’ila Uba, mutanen su 16 za su gurfana don amsa tuhuma kan wannan zargi bisa tanadin dokokin aikin Soji na Najeriya, yayinda ya ce za a yi hukuncin ne a fayyace bisa tsantsar gaskiya da adalci

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Gwamnan Kano ya sauke shugaban ma’aikatan jihar Alhaji Abdullahi Musa daga mukaminsa

March 11, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

Sojojin UAE biyu sun mutu a hatsarin jirgin sama – Ma’aikatar tsaro

March 10, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026

Mojtaba Khamenei Ya Gaji Mahaifinsa A Matsayin Jagoran Addinin Iran

March 9, 2026

Farashin litar man fetur ya zarce naira dubu 1 a sassan Najeriya

March 9, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Bincike Na Musamman

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

By WafsymMarch 11, 2026

Sabbin matakan da Majalisar Dokokin Jihar Kano ta dauka na fara shirin tsige Mataimakin Gwamna,…

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026

KANO: Farashin Kayan Masarufi Ya Yi Tashin Gwauron Zabi Gabanin Shigowar Azumin Ramadan ‎ ‎

February 12, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.