Hukumar Shirya Jarrabawar Shiga Manyan Makarantu ta Ƙasa (JAMB) ta sanar cewa rajistar UTME 2026 za ta fara ne daga Litinin, 26 ga Janairu, zuwa 28 ga Fabrairu, a dukkan cibiyoyin kwamfuta (CBT) da hukumar ta amince da su a fadin Najeriya.
Shugaban JAMB, Farfesa Ishaq Oloyede, ya bayyana haka ne a Legas yayin taro da Kwamishinonin Ilimi na jihohi. Ya ce sayar da takardar neman rajista (e-PIN) zai fara daga 19 ga Janairu kafin fara rajistar kai tsaye.
Farfesa Oloyede ya kara da cewa zaɓin jarabawar gwaji (mock) zai rufe a ranar 16 ga Fabrairu, yayin da sayar da takardun neman Direct Entry (DE) zai fara daga 2 ga Maris har zuwa 25 ga Afrilu.
Shugaban hukumar ya yi gargadi cewa duk cibiyoyin CBT da ba a iya sa ido a kansu daga hedkwatar JAMB ba za su samu biyan kuɗi, kuma rajistarsu na iya soke wa. Haka nan, ɗalibai ba su da bukatar biyan kowanne ƙarin kuɗi ga cibiyoyin CBT; kuɗin rajista da JAMB ta amince da su kaɗai ake biya.
Ya shawarci ɗalibai su yi rajista da wuri domin samun garuruwan da suka fi so, tare da bayyana duk wani tarihi na rajista ko shiga makaranta da suka taɓa yi, domin kaucewa laifukan rashin gaskiya.
Game da shekarun shiga, JAMB ta ce ɗaliban da za su cika shekara 16 zuwa 30 ga Satumba, 2026, su ne suka cancanci UTME, yayin da ‘yan ƙasa da shekarun za su fuskanci tsauraran gwaje-gwaje na musamman kafin a ba su rangwamen shiga.

