Shugaban Jam’iyyar NNPP mai kayan marmari na jihar Kano, Sanata Mas’ud El-Jibril Doguwa, ya yi Allah-wadai da kisan matar aure da ’ya’yanta shida a Jihar Kano.
An kashe Fatima Abubakar mai shekaru 35, tare da ’ya’yanta a gidansu da ke Dorayi Gidan Kwari a ranar Juma’a.
Rikicin Cikin Gida Ne Zai Iya Tura Abba Kabir Yusuf Barin NNPP — Shugaban Jam’iyyar a Kano
Sanata Doguwa ya yi wannan bayani ne yayin wani taron “Manema Labari” da aka gudanar a Kano ya bayyana lamarin a matsayin abun tashin hankali, kuma ya ce lamarin ya taɓa zuciyar al’ummar Kano.
“Na shiga matuƙar damuwa da girgiza bisa kisan gillar da aka yi wa wata uwa da ’ya’yanta shida a Kano.
“Wannan mugun aiki bai tsaya kan waɗannan mutane ba, ya karya tasirinmu na zaman lafiya da girmama rayuwar ɗan Adam,” in ji shi.
Shugaban Jam’iyyar ya kuma miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan marigayiyar da sauran waɗanda lamarin ya shafa, tare da yin addu’a ga mamatan.
“Ina miƙa ta’aziyyata ga iyalan mamatan, da al’ummar Dorayi da Chiranchi, da kuma ɗaukacin al’ummar Jihar Kano.
“Allah Ya gafarta musu, Ya bai wa iyalansu haƙuri da juriyar jure wannan babban rashi,” in ji shi.
Ya kuma yi kira ga gwamnati, hukumomin tsaro, sarakunan gargajiya da shugabanni da su haɗa kai wajen kare rayuka da hana aukuwar irin wannan lamari a nan gaba.

