Shugaban Jam’iyyar NNPP mai kayan marmari na jihar Kano, Sanata Mas’ud El-Jibril Doguwa, ya bayyana cewa rikice-rikicen cikin gida da suka addabi jam’iyyar ne ka iya zama babban dalilin da zai sa Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya fice daga jam’iyyar.
Sanata Doguwa ya yi wannan bayani ne yayin wani taron “Menene Labari” da aka gudanar a Kano, inda ya ce matsalolin cikin gida sun yi matuƙar tsanani, tare da haddasa rarrabuwar kai a tsakanin shugabanni da mambobin jam’iyyar.
Sarki Sunusi II Ya Bukaci Hukuncin Kisa Kan Masu Kashe Mutanen da Ba Su Ji Ba, Ba Su Gani Ba a Kano
A cewarsa, rashin daidaito a tsarin tafiyar da jam’iyyar, rikicin shugabanci da kuma saɓanin ra’ayi tsakanin NNPP da Kwankwasiyya sun jefa jam’iyyar cikin wani yanayi na ruɗani, wanda hakan ke barazana ga makomar ta a Kano da ma ƙasa baki ɗaya.
“Idan ba a gaggauta magance waɗannan matsaloli ba, akwai yiwuwar manyan ’ya’yan jam’iyyar, ciki har da Gwamna Abba Kabir Yusuf, su fara tunanin sauya sheƙa,” in ji Doguwa.
Ya ƙara da cewa gwamnan na fuskantar matsin lamba daga bangarori daban-daban na jam’iyyar, wanda hakan ke iya shafar aikin gwamnati da kuma manufofin da ya sanya gaba tun bayan hawansa mulki.
Sai dai har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, Gwamna Abba Kabir Yusuf bai fito ya tabbatar ko ya musanta yiwuwar barin jam’iyyar NNPP ba.
Masana harkokin siyasa na ganin cewa rikice-rikicen cikin gida na iya zama barazana ga jam’iyyun siyasa, musamman idan ba a shawo kansu cikin hikima da adalci ba, domin hakan na iya haifar da sauya sheƙa da sauyin tsarin siyasa a yankuna.

