Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Gwamnatin jihar Kano ta umarci masu gudanar da sana’ar gwangwan da su dakatar da sayo kayayyakin daga yankin Arewa maso Gabas
Kano

Gwamnatin jihar Kano ta umarci masu gudanar da sana’ar gwangwan da su dakatar da sayo kayayyakin daga yankin Arewa maso Gabas

July 2, 2025
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn

Gwamnatin jihar kano ta umarci masu gudanar da sana’ar gwangwan dake jihar kano da su dakatar da sayo kayayyakin gwangwan daga yankin Arewa maso Gabas na ƙasar nan sakamakon iftila’in da aka samu a jihar nan a kwanan nan kan yadda aka samu abubuwan fashewa a jihar sanadiyyar kayan gwangwan da suke da alaƙa da yankin Arewa maso gabas ɗin ƙasar nan.

Kwamishinan tsaro na jihar kano AVM Ibrahim Umaru mai ritaya ne ya bayyana hakan a yau yayin wata ganawa da ƙungiyar masu sana’ar gwangwan na ƙasa reshen Arewa kan irin iftila’in da ya fara a jihar Kano a lokutan nan sanadiyyar kayan gwangwan.

Avm Ibrahim Umaru ya ƙara da cewa an ɗauki wannan matakin ne domin kare rayukan da dukiyoyin al’ummar jihar Kano.

Da yake jawabi shugaban ƙungiyar masu sayar da kayan gwangwan na yankin Arewa Alhaji Aminu Hassan yace sun gamsu da wannan umarnin da gwamnatin kano ta bayar na dakatar da shigo da kayan gwangwan daga yankin Arewa maso Gabas domin kare jihar kano daga barazanar tsaro.

Wakilin mu ya rawaito cewa Kwamishinan ya kuma gargadi ƙungiyar da su kasance masu bin umarnin da aka basu domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Yadda dawowar sanyi ya sauya al’amura a Kano

January 12, 2026

Majalisar Dokokin Legas Ta Amince Da Kasafin Kuɗin 2026 Na Naira Tiriliyan 4.4

January 9, 2026

Yan siyasan Arewa da malaman addinin Arewa da sarakunan Arewa su ne suka sayar da Arewa ‎ ‎—Naja’atu Muhammad

December 31, 2025

Sheikh gumi ya soki farmakin saman Amurka a Najeriya

December 26, 2025

’Yan majalisar dokokin Kano 2 sun rasu

December 24, 2025

Jinkirin aiwatar da dokokin haraji zai cutar da ma’aikata da talakawa — shugaban kwamitin fadar shugaban ƙasa 

December 22, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsohon Gwamna Na Fuskantar Bincike Kan Zargin Hannu a Shirin Juyin Mulki

By WafsymOctober 20, 2025

Rahotanni sun bayyana cewa tsohon gwamna daga wani yanki na kudu na ƙasar nan wanda…

Hawan Jini: Ƙungiyoyi Sun Yi Gargadi Kan Yaduwar Cutar a Nijeriya

September 27, 2025

Barkewar Cututtuka Uku Sun Tayar da Hankalin Hukumomin Lafiya a Nijeriya ‎

September 27, 2025

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

April 13, 2025
© 2026 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.