Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » NDLEA da NAPTIP Zasu Ƙarfafa Haɗin Gwiwa don Yaƙi da Safarar Miyagun Kwayoyi da Mutane
Afrika

NDLEA da NAPTIP Zasu Ƙarfafa Haɗin Gwiwa don Yaƙi da Safarar Miyagun Kwayoyi da Mutane

April 25, 2025
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
NDLEA LOGO

Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi (NDLEA) tare da Hukumar Hana Fataucin Mutane (NAPTIP) sun kafa wata rundunar jami’an su domin hada karfi tare wajen yaƙi da safarar miyagun kwayoyi da safarar mutane.

Wannan mataki ya fito ne a lokacin da Shugabar NAPTIP, Binta Lami Adamu Bello, ta kai ziyarar girmamawa ga Shugaban NDLEA, na Kasa Birgediya Janar Mohammed Buba Marwa, mai ritaya a hedikwatar NDLEA dake Abuja, yau jumma’a 25 ga Afrilu, 2025.

A cikin jawabinsa, Marwa ya taya Binta Adamu Bello, murna bisa nadinta da shugaban Kasa Bola Ahamad Tunibu,yayi kuma ya yaba da yadda ta soma aiki da ƙwazo.
Ta cikin wata sanarwa da daraktan Yaɗa labarai da wayar daa kan jamma’a a hukumar Femi Baba Femi,Yafitar Ya bayyana cewa akwai alaƙa tsakanin safarar mutane da safarar miyagun kwayoyi, inda wasu daga cikin waɗanda ake safararsu ke zama masu ɗaukar kwayoyi ba tare da saninsu ba.
Sanarwar ta kara da cewa akwai bukatar haɗin gwiwa ta hanyar sanya hannu kan yarjejeniya (MoU) da za ta fayyace fannoni na aiki tare.

A nata bangaren, Shugabar yaki da safarar mutane da cin zarafin kananan Yara NAPTIP ta Kasa Binta Lami Adamu Bello, ta bayyana cewa akwai buƙatar haɗin kai sosai tsakanin hukumomin biyu domin toshe hanyoyin aikata laifukan, musamman ganin yadda ammfani da kananan Yara da Mata wajen safarar kwayoyi, sannan a kan yi musu allura ko a basu kwayoyi domin su kasance masu biyayya.

Ta kuma jaddada cewa laifukan biyu nafaruwa ne a iyakoki marasa tsaro, rashawa, talauci, da raunin hukumomi. Ta ce akwai buƙatar gina tsarin aiki na haɗin gwiwa wanda zai haɗa da bincike da musayar bayanan sirri, horas da ma’aikata tare, amfani da fasaha da bayanai, wayar da kai ga jama’a, da kuma yin garambawul ga dokoki.

Hukumomin sun amince da kafa shirin aiki na NDLEA da NAPTIP na lokaci gajere zuwa matsakaici, da gudanar da taron duba ayyuka sau ɗaya ko biyu a shekara, da kuma inganta haɗin gwiwa da ƙungiyoyi na ƙasa da ƙasa.

Featured
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Kwalejin Ilimi ta Isa Kaita dake Karamar Hukumar Dutsenma a Jihar Katsina ta tuna da Marigayi Isa Kaita

July 2, 2025

Da gudu zan karɓi tayin kujerar mataimakin shugaban Najeriya – Barau I Jibrin

June 26, 2025

Hatsaniyar data Faru a Karamar Hukumar Rano wadda ta kai ga Rasuwar DPO da wani mutum daya– ‘Yan sanda Sun Nemi Hadin kai don Dawo da Tsaro a Yankin

May 27, 2025

Babbar kotun shariar musulunci ta yankewa matashin nan Shafiu Abubakar hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan samunsa da laifin kashe wasu mutane

May 27, 2025

Hukumar tace fina-finai ta yi nasarar kama wasu na’urori da ake amfani dasu wajan buga hotunan batsa ga masu sana’ar maganin Gargajiya a Jahar Kano

May 26, 2025

Babbar Kotun Tarayya ta yi umarni ga Hukumar EFCC data cigaba da bincike kan filin Musabaka da ake zargin wasu a Jihar Kano sun siyar ba bisa ka’ida ba

May 23, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Kano

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

By WafsymApril 13, 2025

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta bayana Dalilan yin Gwanjon…

Hukumar tace fina-finai ta haramtawa Usman Sojaboy da wasu mata biyu shiga harkokin Film ko waka a Kano

January 20, 2025

Madrid ko Barca: Wa zai lashe Spanish Super Cup?

January 12, 2025

Barca ta kara rashin nasarar ɗaukaka kara kan yi wa Olmo rijista

December 31, 2024
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.