Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Jami’an tsaro sun harbe mutane 4 tare da jikkata wasu 16 yayin rushe wasu Gidaje da Kwangaye a Kano
Afrika

Jami’an tsaro sun harbe mutane 4 tare da jikkata wasu 16 yayin rushe wasu Gidaje da Kwangaye a Kano

February 3, 2025
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
WhatsApp Image 2025 02 03 at 15.55.43

Ana zargin Jami’an tsaro da harbe mutane huɗu tare da jikkata wasu 16, yayin atisayen rushe gine-gine da gwamnatin jihar Kano dake arewacin Najeriya ta gudanar a garin Rimin Zakara, dake kusa da Jami’ar Bayero ta Kano a ƙaramar hukumar Ungogo a jihar.

Aikin na rusau ɗin ya shafi gine-gine kimanin 18.

Al’amarin ya faru ne adaren lahadi, lamarin da ya haifar da turjiya daga mazauna yankin, inda suka ce ba a basu isasshiyar sanarwa ba kafin rushewar.

Malam Sunusi Dan-Baba, ganau ne ya shaida cewa tawagar rusau ta iso da daddare, inda suka fara ruguza gidaje da shaguna.

Ya ƙara da cewa ana takaddama kan mallakar filin unguwar tsakanin jami’ar Bayero ta Kano da mazauna yankin sama da shekaru 20 da suka gabata.

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar tsaro da kare kadarorin gwamnati (NSCDC) reshen Jihar Kano, Ibrahim Abdullahi, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa an tura jami’an tsaro ne domin kare kadarorin gwamnati, sai mazauna yankin suka kai musu farmaki, inda suka raunata jami’i ɗaya, tare da lalata motocin su.

A bangaren ma’aikatar filaye da tsare-tsare ta jihar Kano, ta tabbatar da cewa filin na Jami’ar Bayero ne, kuma an bi duk hanyoyin doka kafin rusau din.

Daraktan yada labarai na ma’aikatar, Umar Abdu Kurmawa, ya ce an bayar da sanarwa tun kafin aiwatar da rusau din, har ma an biya diyya ga wadanda abin ya shafa sama da shekaru 20 da suka wuce.

Duk kokarin jin ta bakin Daraktan Hulda da Jama’a na Jami’ar Bayero, Malam Lamara Garba, bai yi nasara ba, domin wayarsaa  a kashe take.

Featured
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Kwalejin Ilimi ta Isa Kaita dake Karamar Hukumar Dutsenma a Jihar Katsina ta tuna da Marigayi Isa Kaita

July 2, 2025

Da gudu zan karɓi tayin kujerar mataimakin shugaban Najeriya – Barau I Jibrin

June 26, 2025

Hatsaniyar data Faru a Karamar Hukumar Rano wadda ta kai ga Rasuwar DPO da wani mutum daya– ‘Yan sanda Sun Nemi Hadin kai don Dawo da Tsaro a Yankin

May 27, 2025

Babbar kotun shariar musulunci ta yankewa matashin nan Shafiu Abubakar hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan samunsa da laifin kashe wasu mutane

May 27, 2025

Hukumar tace fina-finai ta yi nasarar kama wasu na’urori da ake amfani dasu wajan buga hotunan batsa ga masu sana’ar maganin Gargajiya a Jahar Kano

May 26, 2025

Babbar Kotun Tarayya ta yi umarni ga Hukumar EFCC data cigaba da bincike kan filin Musabaka da ake zargin wasu a Jihar Kano sun siyar ba bisa ka’ida ba

May 23, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Kano

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

By WafsymApril 13, 2025

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta bayana Dalilan yin Gwanjon…

Hukumar tace fina-finai ta haramtawa Usman Sojaboy da wasu mata biyu shiga harkokin Film ko waka a Kano

January 20, 2025

Madrid ko Barca: Wa zai lashe Spanish Super Cup?

January 12, 2025

Barca ta kara rashin nasarar ɗaukaka kara kan yi wa Olmo rijista

December 31, 2024
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.