Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Jami’an tsaro sun harbe mutane 4 tare da jikkata wasu 16 yayin rushe wasu Gidaje da Kwangaye a Kano
Afrika

Jami’an tsaro sun harbe mutane 4 tare da jikkata wasu 16 yayin rushe wasu Gidaje da Kwangaye a Kano

February 3, 2025
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
WhatsApp Image 2025 02 03 at 15.55.43

Ana zargin Jami’an tsaro da harbe mutane huɗu tare da jikkata wasu 16, yayin atisayen rushe gine-gine da gwamnatin jihar Kano dake arewacin Najeriya ta gudanar a garin Rimin Zakara, dake kusa da Jami’ar Bayero ta Kano a ƙaramar hukumar Ungogo a jihar.

Aikin na rusau ɗin ya shafi gine-gine kimanin 18.

Al’amarin ya faru ne adaren lahadi, lamarin da ya haifar da turjiya daga mazauna yankin, inda suka ce ba a basu isasshiyar sanarwa ba kafin rushewar.

Malam Sunusi Dan-Baba, ganau ne ya shaida cewa tawagar rusau ta iso da daddare, inda suka fara ruguza gidaje da shaguna.

Ya ƙara da cewa ana takaddama kan mallakar filin unguwar tsakanin jami’ar Bayero ta Kano da mazauna yankin sama da shekaru 20 da suka gabata.

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar tsaro da kare kadarorin gwamnati (NSCDC) reshen Jihar Kano, Ibrahim Abdullahi, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa an tura jami’an tsaro ne domin kare kadarorin gwamnati, sai mazauna yankin suka kai musu farmaki, inda suka raunata jami’i ɗaya, tare da lalata motocin su.

A bangaren ma’aikatar filaye da tsare-tsare ta jihar Kano, ta tabbatar da cewa filin na Jami’ar Bayero ne, kuma an bi duk hanyoyin doka kafin rusau din.

Daraktan yada labarai na ma’aikatar, Umar Abdu Kurmawa, ya ce an bayar da sanarwa tun kafin aiwatar da rusau din, har ma an biya diyya ga wadanda abin ya shafa sama da shekaru 20 da suka wuce.

Duk kokarin jin ta bakin Daraktan Hulda da Jama’a na Jami’ar Bayero, Malam Lamara Garba, bai yi nasara ba, domin wayarsaa  a kashe take.

Featured
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Yadda dawowar sanyi ya sauya al’amura a Kano

January 12, 2026

Majalisar Dokokin Legas Ta Amince Da Kasafin Kuɗin 2026 Na Naira Tiriliyan 4.4

January 9, 2026

Yan siyasan Arewa da malaman addinin Arewa da sarakunan Arewa su ne suka sayar da Arewa ‎ ‎—Naja’atu Muhammad

December 31, 2025

Sheikh gumi ya soki farmakin saman Amurka a Najeriya

December 26, 2025

Jinkirin aiwatar da dokokin haraji zai cutar da ma’aikata da talakawa — shugaban kwamitin fadar shugaban ƙasa 

December 22, 2025

An Kama ‘Yan Mata Biyu da Laifin Yunkurin Shigar da Miyagun Kwayoyi Cikin Gidan Yari a Kano

December 22, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsohon Gwamna Na Fuskantar Bincike Kan Zargin Hannu a Shirin Juyin Mulki

By WafsymOctober 20, 2025

Rahotanni sun bayyana cewa tsohon gwamna daga wani yanki na kudu na ƙasar nan wanda…

Hawan Jini: Ƙungiyoyi Sun Yi Gargadi Kan Yaduwar Cutar a Nijeriya

September 27, 2025

Barkewar Cututtuka Uku Sun Tayar da Hankalin Hukumomin Lafiya a Nijeriya ‎

September 27, 2025

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

April 13, 2025
© 2026 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.