Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Jami’an tsaro sun harbe mutane 4 tare da jikkata wasu 16 yayin rushe wasu Gidaje da Kwangaye a Kano
Afrika

Jami’an tsaro sun harbe mutane 4 tare da jikkata wasu 16 yayin rushe wasu Gidaje da Kwangaye a Kano

February 3, 2025
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
WhatsApp Image 2025 02 03 at 15.55.43

Ana zargin Jami’an tsaro da harbe mutane huɗu tare da jikkata wasu 16, yayin atisayen rushe gine-gine da gwamnatin jihar Kano dake arewacin Najeriya ta gudanar a garin Rimin Zakara, dake kusa da Jami’ar Bayero ta Kano a ƙaramar hukumar Ungogo a jihar.

Aikin na rusau ɗin ya shafi gine-gine kimanin 18.

Al’amarin ya faru ne adaren lahadi, lamarin da ya haifar da turjiya daga mazauna yankin, inda suka ce ba a basu isasshiyar sanarwa ba kafin rushewar.

Malam Sunusi Dan-Baba, ganau ne ya shaida cewa tawagar rusau ta iso da daddare, inda suka fara ruguza gidaje da shaguna.

Ya ƙara da cewa ana takaddama kan mallakar filin unguwar tsakanin jami’ar Bayero ta Kano da mazauna yankin sama da shekaru 20 da suka gabata.

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar tsaro da kare kadarorin gwamnati (NSCDC) reshen Jihar Kano, Ibrahim Abdullahi, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa an tura jami’an tsaro ne domin kare kadarorin gwamnati, sai mazauna yankin suka kai musu farmaki, inda suka raunata jami’i ɗaya, tare da lalata motocin su.

A bangaren ma’aikatar filaye da tsare-tsare ta jihar Kano, ta tabbatar da cewa filin na Jami’ar Bayero ne, kuma an bi duk hanyoyin doka kafin rusau din.

Daraktan yada labarai na ma’aikatar, Umar Abdu Kurmawa, ya ce an bayar da sanarwa tun kafin aiwatar da rusau din, har ma an biya diyya ga wadanda abin ya shafa sama da shekaru 20 da suka wuce.

Duk kokarin jin ta bakin Daraktan Hulda da Jama’a na Jami’ar Bayero, Malam Lamara Garba, bai yi nasara ba, domin wayarsaa  a kashe take.

Featured
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Hukumomin yaƙi da cin hanci ba su taɓa gayyata ta ba — Pantami

April 14, 2026

An kama jami’an ƴansanda 6 tare da wasu mutane 3 bisa zargin ƙwace da satar mutane a Edo 

April 14, 2026

Maki shida ne ya rage tsakanin Arsenal da Man City

April 13, 2026

Mutane sama da 50 sun rasu a kuskuren harin sojin sama a kasuwa

April 13, 2026

INEC ta ɗage aikin sabunta bayanan rajistar masu zaɓe a fadin ƙasa

April 11, 2026

Gwamnan Kano ya naɗa Bilkisu Maimota a matsayin shugabar ma’aikata ta jiha

April 11, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

By WafsymApril 2, 2026

A Jihar Kano, ana ci gaba da nuna damuwa kan yadda wasu masu anfani da…

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.