Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Daga 2025 Najeriya zata fara hako gangar mai miliyan 3 a kowace rana – Heineken Lokpobiri
Afrika

Daga 2025 Najeriya zata fara hako gangar mai miliyan 3 a kowace rana – Heineken Lokpobiri

December 31, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn

Gwamnatin Nijeriya ta ƙara ƙaimi wajen yaƙi da ɓarayin man fetur a yankin Neja Delta a yayin da take shirin fitar da gangar mai miliyan 3 a kowace rana a shekarar 2025.

Nijeriya wadda ke cikin ƙasashen da ke kan gaba wajen fitar da ɗanyen fetur a Afirka, ta na samun yawancin kuɗin shigarta daga mai, kuma tana samun fiye da kashi 90 na kuɗaɗen ƙasashen waje daga sayar da man fetur, amma tana fama da ɓarayin mai.

A yayin da gwamnatin ƙasar ta yi ƙiyasin fitar da ganga miliyan 2.06 ta man fetur a kasafin kuɗinta na shekara mai zuwa, a zahiri fetur ɗin da take fitarwa bai wuce ganga miliyan 1.8 a kowace rana ba, a cewar alƙaluman da hukumomi suka fitar.

Ma’aikatar man fetur da rundunar sojin sama ta Nijeriya sun ƙaddamar da yaƙi da ɓarayin danyen fetur, mai suna Delta Sanity a shekarar da ta wuce.

Babban Hafsan sojin saman ƙasar Emmanuel Ogalla ya ce yanzu shiri na OPDS ya shiga zango na biyu, inda za su yi amfani da jirage marasa matuƙa da helikwafta da ƙarin jami’an leƙen asiri wajen ganin sun rage matsalar, inda suke sa rai za a riƙa fitar da ɗanyen mai da ya kai ganga miliyan uku a kowace rana.

“Idan ka dubi yadda lamura suke a bara, lokacin da muka ƙaddamar da wannan shiri, muna samun gangar ɗanyen fetur miliyan 1.4 kowace rana. Yanzu ya ƙaru zuwa ganga miliyan 1.8.

“Na yi amanna cewa idan muka kammala ɗaukar wadannan matakai, za mu cim ma manufarmu ko ma mu haura ƙiyasin da muka yi,” a cewar Ogalla a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata bayan ya ƙaddamar da sabon shirin yaƙi da ɓarayin ɗanyen man fetur a Fatakwal babban birnin Jihar Ribas.

Ƙaramin Ministan Harkokin Man Fetur Heineken Lokpobiri ya ce adadin ɗanyen fetur ɗin da Nijeriya take fitarwa da kaɗan ya wuce ganga miliyan 1 a kowace rana lokacin da ya soma aiki a watan Agustan 2023.

“Burinmu shi ne mu riƙa fitar da ganga miliyan 3 a kowace rana daga yanzu zuwa shekarar 2025 kuma muna da ƙwarin gwiwa cewa ƙaddamar da yaƙi da ɓarayin mai da muka yi a zango na biyu, wato OPDS zai taka muhimmiyar rawa” Inji Heineken

Featured
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Kwalejin Ilimi ta Isa Kaita dake Karamar Hukumar Dutsenma a Jihar Katsina ta tuna da Marigayi Isa Kaita

July 2, 2025

Da gudu zan karɓi tayin kujerar mataimakin shugaban Najeriya – Barau I Jibrin

June 26, 2025

Hatsaniyar data Faru a Karamar Hukumar Rano wadda ta kai ga Rasuwar DPO da wani mutum daya– ‘Yan sanda Sun Nemi Hadin kai don Dawo da Tsaro a Yankin

May 27, 2025

Babbar kotun shariar musulunci ta yankewa matashin nan Shafiu Abubakar hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan samunsa da laifin kashe wasu mutane

May 27, 2025

Hukumar tace fina-finai ta yi nasarar kama wasu na’urori da ake amfani dasu wajan buga hotunan batsa ga masu sana’ar maganin Gargajiya a Jahar Kano

May 26, 2025

Babbar Kotun Tarayya ta yi umarni ga Hukumar EFCC data cigaba da bincike kan filin Musabaka da ake zargin wasu a Jihar Kano sun siyar ba bisa ka’ida ba

May 23, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Kano

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

By WafsymApril 13, 2025

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta bayana Dalilan yin Gwanjon…

Hukumar tace fina-finai ta haramtawa Usman Sojaboy da wasu mata biyu shiga harkokin Film ko waka a Kano

January 20, 2025

Madrid ko Barca: Wa zai lashe Spanish Super Cup?

January 12, 2025

Barca ta kara rashin nasarar ɗaukaka kara kan yi wa Olmo rijista

December 31, 2024
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.