Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Zarge-zargen Shugaban mulkin Sojin Nijar ba su da tushe balle makama – Gwamnatin Nijeriya
Afrika

Zarge-zargen Shugaban mulkin Sojin Nijar ba su da tushe balle makama – Gwamnatin Nijeriya

December 26, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta yi fatali da zarge-zargen da shugaban mulkin sojin Nijar, Janar Abdourahamane Tchiani ya yi kan cewa Nijeriya da Faransa suna ƙoƙarin tayar da hargitsi a ƙasarsa.

Sanarwa da Ministan yada Labaran gwamnatin Nijeriya, Mohammed Idris ya fitar ranar Alhamis ta ce “Wadannan zarge-zarge dai sun wanzu ne kawai a tunani, domin Nijeriya ba ta taba kulla wata alaka da a bayyane ko a boye da Faransa ba – ko wata kasa – domin daukar nauyin hare-haren ta’addanci ko ta da hargitsi a Jamhuriyar Nijar sakamakon sauyin mulkin da aka samu a shugabancin kasar.”

Sanarwar ta ci gaba da cewa Shugaba Tinubu a matsayinsa na shugaban ƙungiyar ECOWAS, ya nuna jagoranci na gari, “tare da bude kofofin kananan ƙungiyoyin yanki domin sake shigar jamhuriyar Nijar cikin al’amura duk da halin da kasar ke ciki a siyasance.

“Nijeriya na ci gaba da jajircewa wajen samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da kuma alakar diflomasiya mai dimbin tarihi da Nijar,” in ji sanarwar gwamnatin.

Tun da fari Shugaban Nijar Janar Abdourahamane Tiani ne ya fada a wata hira da kafar yada labaran kasarsa cewa sun jima da bai wa gwamnatin Nijeriya bayanan sirri game da yadda Faransa take shirin kafa sansanin ‘yan ta’adda na ƙungiyar Lakurawa a arewacin Nijeriya.

Janar Tiani ya yi zargin cewa gwamnatin Nijeriya na da masaniya game da ayyukan Lakurawa da kuma yin watsi da shawarwarin da suka ba ta game da ‘yan ta’addan.

Minista Mohammed Idris ya ƙara da cewa Rundunar Sojin Nijeriya tare da hadin guiwar takwarorinta na rundunar hadin gwiwa ta kasa da kasa, na samun nasarar dakile ayyukan ta’addanci a yankin.

“Don haka, shirme ne a ce Nijeriya za ta hada baki da duk wani karfi na kasashen waje domin kawo cikas ga zaman lafiya da tsaron wata kasa makwabciyarta.”

Tun bayan juyin mulkin da aka yi a Nijar a shekarar 2023 alaƙa tsakanin ƙasashen biyun maƙwabtan juna ke ta yin tsami, lamarin da har ya kai ga Nijar barazanar ficewa daga ƙungiyar ECOWAS, wadda Tinubu na Nijeriya ke jagoranta.

Maitaimakawa shugaban Najeriya kan harkokin yaɗa labarai Abdulaziz Abdulaziz shima ya ce babu gaskiya a zarge zargen shugaban na Niger.

Featured
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Gwamnan Kano ya sauke shugaban ma’aikatan jihar Alhaji Abdullahi Musa daga mukaminsa

March 11, 2026

Sojojin UAE biyu sun mutu a hatsarin jirgin sama – Ma’aikatar tsaro

March 10, 2026

Mojtaba Khamenei Ya Gaji Mahaifinsa A Matsayin Jagoran Addinin Iran

March 9, 2026

Farashin litar man fetur ya zarce naira dubu 1 a sassan Najeriya

March 9, 2026

Mutanen da ake hasashen za su maye gurbin Mataimakin Gwamnan Kano

March 7, 2026

Yakin Amurka/Isra’ila da Iran: Lallai da ni za a zaɓi sabon shugaba a Iran – Trump

March 6, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Bincike Na Musamman

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

By WafsymMarch 11, 2026

Sabbin matakan da Majalisar Dokokin Jihar Kano ta dauka na fara shirin tsige Mataimakin Gwamna,…

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026

KANO: Farashin Kayan Masarufi Ya Yi Tashin Gwauron Zabi Gabanin Shigowar Azumin Ramadan ‎ ‎

February 12, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.