Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Zarge-zargen Shugaban mulkin Sojin Nijar ba su da tushe balle makama – Gwamnatin Nijeriya
Afrika

Zarge-zargen Shugaban mulkin Sojin Nijar ba su da tushe balle makama – Gwamnatin Nijeriya

December 26, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta yi fatali da zarge-zargen da shugaban mulkin sojin Nijar, Janar Abdourahamane Tchiani ya yi kan cewa Nijeriya da Faransa suna ƙoƙarin tayar da hargitsi a ƙasarsa.

Sanarwa da Ministan yada Labaran gwamnatin Nijeriya, Mohammed Idris ya fitar ranar Alhamis ta ce “Wadannan zarge-zarge dai sun wanzu ne kawai a tunani, domin Nijeriya ba ta taba kulla wata alaka da a bayyane ko a boye da Faransa ba – ko wata kasa – domin daukar nauyin hare-haren ta’addanci ko ta da hargitsi a Jamhuriyar Nijar sakamakon sauyin mulkin da aka samu a shugabancin kasar.”

Sanarwar ta ci gaba da cewa Shugaba Tinubu a matsayinsa na shugaban ƙungiyar ECOWAS, ya nuna jagoranci na gari, “tare da bude kofofin kananan ƙungiyoyin yanki domin sake shigar jamhuriyar Nijar cikin al’amura duk da halin da kasar ke ciki a siyasance.

“Nijeriya na ci gaba da jajircewa wajen samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da kuma alakar diflomasiya mai dimbin tarihi da Nijar,” in ji sanarwar gwamnatin.

Tun da fari Shugaban Nijar Janar Abdourahamane Tiani ne ya fada a wata hira da kafar yada labaran kasarsa cewa sun jima da bai wa gwamnatin Nijeriya bayanan sirri game da yadda Faransa take shirin kafa sansanin ‘yan ta’adda na ƙungiyar Lakurawa a arewacin Nijeriya.

Janar Tiani ya yi zargin cewa gwamnatin Nijeriya na da masaniya game da ayyukan Lakurawa da kuma yin watsi da shawarwarin da suka ba ta game da ‘yan ta’addan.

Minista Mohammed Idris ya ƙara da cewa Rundunar Sojin Nijeriya tare da hadin guiwar takwarorinta na rundunar hadin gwiwa ta kasa da kasa, na samun nasarar dakile ayyukan ta’addanci a yankin.

“Don haka, shirme ne a ce Nijeriya za ta hada baki da duk wani karfi na kasashen waje domin kawo cikas ga zaman lafiya da tsaron wata kasa makwabciyarta.”

Tun bayan juyin mulkin da aka yi a Nijar a shekarar 2023 alaƙa tsakanin ƙasashen biyun maƙwabtan juna ke ta yin tsami, lamarin da har ya kai ga Nijar barazanar ficewa daga ƙungiyar ECOWAS, wadda Tinubu na Nijeriya ke jagoranta.

Maitaimakawa shugaban Najeriya kan harkokin yaɗa labarai Abdulaziz Abdulaziz shima ya ce babu gaskiya a zarge zargen shugaban na Niger.

Featured
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Kwalejin Ilimi ta Isa Kaita dake Karamar Hukumar Dutsenma a Jihar Katsina ta tuna da Marigayi Isa Kaita

July 2, 2025

Da gudu zan karɓi tayin kujerar mataimakin shugaban Najeriya – Barau I Jibrin

June 26, 2025

Hatsaniyar data Faru a Karamar Hukumar Rano wadda ta kai ga Rasuwar DPO da wani mutum daya– ‘Yan sanda Sun Nemi Hadin kai don Dawo da Tsaro a Yankin

May 27, 2025

Babbar kotun shariar musulunci ta yankewa matashin nan Shafiu Abubakar hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan samunsa da laifin kashe wasu mutane

May 27, 2025

Hukumar tace fina-finai ta yi nasarar kama wasu na’urori da ake amfani dasu wajan buga hotunan batsa ga masu sana’ar maganin Gargajiya a Jahar Kano

May 26, 2025

Babbar Kotun Tarayya ta yi umarni ga Hukumar EFCC data cigaba da bincike kan filin Musabaka da ake zargin wasu a Jihar Kano sun siyar ba bisa ka’ida ba

May 23, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Kano

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

By WafsymApril 13, 2025

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta bayana Dalilan yin Gwanjon…

Hukumar tace fina-finai ta haramtawa Usman Sojaboy da wasu mata biyu shiga harkokin Film ko waka a Kano

January 20, 2025

Madrid ko Barca: Wa zai lashe Spanish Super Cup?

January 12, 2025

Barca ta kara rashin nasarar ɗaukaka kara kan yi wa Olmo rijista

December 31, 2024
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.