Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Gwamnatin Nijeriya ta janye dokar hana haƙar ma’adinai a Zamfara bayan shekaru biyar da kafawa
Afrika

Gwamnatin Nijeriya ta janye dokar hana haƙar ma’adinai a Zamfara bayan shekaru biyar da kafawa

December 23, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn

Gwamnatin Nijeriya ta janye dokar hana haƙar ma’adinai da ta sanya a jihar Zamfara da ke arewacin ƙasar bayan shekaru biyar da kafa dokar.

Ministan haɓaka harkokin ma’adinai, Dele Alake, shi ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai tare kuma da shafinsa na X ranar Lahadi.

Alake ya ce Nijeriya “za ta ci riba mai yawa idan aka ƙara farfaɗo da harkokin tattalin arziƙi a jiha mai ma’adinai da yawa kamar Zamfara wadda take da zinari da lithium da tagulla da yawa.”

“Gwamnatin Tarayya ta ɗage dokar da ta hana haƙar ma’adinai a jihar Zamfara saboda ƙarin sauƙi da aka samu kan lamarin tsaro a faɗin jihar,” in ji sanarwar da ministan ya fitar.

Ministan ya bayyana cewa dokar hana haƙar ma’adinai da aka yi, wadda take da niyya mai kyau, ta bar wani giɓi wanda masu haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’i’da ba suke amfani da shi wajen satar ma’adinan ƙasa.

Ya jaddada cewa jihar tana da yiwuwar samar wa da Nijeriya kuɗin shiga mai tarin yawa.

“Barazana ga rayuka da ta sa aka hana haƙar a shekarar 2019 ta ragu. Manyan nasarorin da jami’an tsaro suka samu sun samar da gagarumar raguwa ga rashin tsaro, kuma yanzu da aka ɗage dokar hana haƙar ma’aidinai, sannu a hankali fannin haƙar ma’adinai na Zamfara zai fara ba da nasa gudunmawar ga kuɗin shigar ƙasa,” a cewar Alake.

“Tun daga farkon gwamnatin Tinubu dai ayyukan jami’a tsaro wadda suke yi bisa bayanan sirri sun yi sanadin kashe manyan ɓarayin daji lamarin da ya rage matsalar tsaro,” in ji ministan.

Acewarsa dage wannan doka zai ba da damar tattara bayanan sirri domin daƙile haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba tare da tabbatar da cewa ƙasar ta amfana da arziƙin ma’adinan jihar.

Alake ya jaddada cewa yarjejeniyar da Nijeriya ta shiga da Faransa da ya janyo ce-ce-ku-ce kwanakin baya ba ya nufin ƙasar za ta sallamar da ma’adananta ko kuma ƙulla alaƙar soji da Faransa.

Featured
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Kwalejin Ilimi ta Isa Kaita dake Karamar Hukumar Dutsenma a Jihar Katsina ta tuna da Marigayi Isa Kaita

July 2, 2025

Da gudu zan karɓi tayin kujerar mataimakin shugaban Najeriya – Barau I Jibrin

June 26, 2025

Hatsaniyar data Faru a Karamar Hukumar Rano wadda ta kai ga Rasuwar DPO da wani mutum daya– ‘Yan sanda Sun Nemi Hadin kai don Dawo da Tsaro a Yankin

May 27, 2025

Babbar kotun shariar musulunci ta yankewa matashin nan Shafiu Abubakar hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan samunsa da laifin kashe wasu mutane

May 27, 2025

Hukumar tace fina-finai ta yi nasarar kama wasu na’urori da ake amfani dasu wajan buga hotunan batsa ga masu sana’ar maganin Gargajiya a Jahar Kano

May 26, 2025

Babbar Kotun Tarayya ta yi umarni ga Hukumar EFCC data cigaba da bincike kan filin Musabaka da ake zargin wasu a Jihar Kano sun siyar ba bisa ka’ida ba

May 23, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Kano

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

By WafsymApril 13, 2025

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta bayana Dalilan yin Gwanjon…

Hukumar tace fina-finai ta haramtawa Usman Sojaboy da wasu mata biyu shiga harkokin Film ko waka a Kano

January 20, 2025

Madrid ko Barca: Wa zai lashe Spanish Super Cup?

January 12, 2025

Barca ta kara rashin nasarar ɗaukaka kara kan yi wa Olmo rijista

December 31, 2024
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.