Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Mun fito da sabbin tsare-tsare da zasu rage kuɗin aikin Hajji a Najeriya – NAHCON
Afrika

Mun fito da sabbin tsare-tsare da zasu rage kuɗin aikin Hajji a Najeriya – NAHCON

December 21, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
WhatsApp Image 2024 12 12 at 14.31.57
WhatsApp Image 2024 12 12 at 14.31.57

Shugaban hukumar Alhaza Najeriya NAHCON Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya ce yanzu haka hukumar ta na cigaba da kai ziyara jihohi da wajan wasu masu ruwa tsaki a faɗin ƙasar ne domin ƙarfafa shirye-shiryen da hukumar ke yi na tsara aikin Hajjin da ya dace a 2025 da kuma bayanta.

Farfesa Abdullahi Saleh ya bayyana hakan ne ranar Juma’a lokacin da ya ziyarci gwamnan jihar Kebbi Dr. Nasir Idris a gidan gwamnatin jihar dake Birnin Kebbi.

Farfesa Pakistan ya lissafo wasu sabbin matakai da hukumarsa ke ɗauka domin ragewa alhazai raɗaɗi a gida da kuma ƙasar Saudi Arabia.

A cewarsa, matakan sun haɗa da yin tunani domin biyan kuɗin aikin Hajji a Naira maimakon dalar Amurka, yana mai cewa, “wannan shi ne zai rage farashin ƙuɗin da ake biya.

Saleh ta yaba da irin goyon bayan da Dr Idris ke ba shi wajen ganin an samu nasarar aikin Hajjin 2025.

“Tare da goyon bayanku da sauran masu ruwa da tsaki, mun himmatu sosai wajen ganin mun kawar da wannan mummunar dabi’a da muka gada a NAHCON.”

Lokacin da yake jawabin, Gwamnan jihar Kebbi Dr. Nasir Idris, ya buƙaci hukumar alhazai ta kasa NAHCON ta ɗauki ƙwararan matakai domin inganta ayyukan hajjin 2025.

Gwamnan ya ce ya tuna da irin ƙalubale iri daban-daban da suka kawo cikas wajen gudanar da ayyukan Hajji na shekarar 2024 da NAHCON ta jagoranta.

Acewar gwamnan ya tuno da irin rashin kyakkyawan shiri da aka yi musamman wajan samar da masauki ga maniyyata da sauran muhimman ayyuka.

Har ilayau ya koka da yadda hukumar ba ta yi jigilar maniyyata yadda ya kamata ba a Makkah da Madina da sauran wurare masu tsarki.

“Ni ma shaida ne a lokacin da na yi aikin Hajjin karshe da kaina tare da wasu gwamnoni da wasu manyan ‘yan Najeriya da alhazanmu suka maƙale aka bar su suna shan wahala” Inji Gwamna Nasir Idris

Dr. Idris ya ce gwamnatinsa ta himmatu wajen tabbatar da gudanar da aikin Hajjin 2025 mai inganci.

“Za mu ci gaba da bayar da tallafin da ake buƙata ga hukumar jin daɗin Alhazai (PWA) da kuma NAHCON ta wannan hanyar kuma ba za mu taɓa yin ƙasa a gwiwa ba,” inji shi.

Shugaban hukumar jin daɗin Alhazai ta jihar Kebbi (PWA), Alhaji Faruk Musa Yero Enabo ya yabawa Dakta Idris bisa yadda ya sanya jihar Kebbi ta zama abin koyi wajen gudanar da ayyukan Hajji a Nigeria.

Ya ce zaɓin da jihar ta yi na ƙaddamar da ziyarar a yankin Arewa maso Yamma ya nuna yadda Dakta Idris ke ci gaba da tallafa wa hukumar sa da kuma ta NAHCON.

Shugaban ya danganta jerin gaggarumin ci gaba da hukumar ta samu da goyon baya da jajircewar Gwamnan.

Ya ƙara da cewa dukkan mahajkatan 2024 kowannensu ya karɓi kudadensa na Naira 61,080, inda gwamnatin jihar ta yi watsi da cajin bankuna daban-daban kamar yadda Dakta Idris ya umarta.

Featured
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Kwalejin Ilimi ta Isa Kaita dake Karamar Hukumar Dutsenma a Jihar Katsina ta tuna da Marigayi Isa Kaita

July 2, 2025

Da gudu zan karɓi tayin kujerar mataimakin shugaban Najeriya – Barau I Jibrin

June 26, 2025

Hatsaniyar data Faru a Karamar Hukumar Rano wadda ta kai ga Rasuwar DPO da wani mutum daya– ‘Yan sanda Sun Nemi Hadin kai don Dawo da Tsaro a Yankin

May 27, 2025

Babbar kotun shariar musulunci ta yankewa matashin nan Shafiu Abubakar hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan samunsa da laifin kashe wasu mutane

May 27, 2025

Hukumar tace fina-finai ta yi nasarar kama wasu na’urori da ake amfani dasu wajan buga hotunan batsa ga masu sana’ar maganin Gargajiya a Jahar Kano

May 26, 2025

Babbar Kotun Tarayya ta yi umarni ga Hukumar EFCC data cigaba da bincike kan filin Musabaka da ake zargin wasu a Jihar Kano sun siyar ba bisa ka’ida ba

May 23, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Kano

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

By WafsymApril 13, 2025

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta bayana Dalilan yin Gwanjon…

Hukumar tace fina-finai ta haramtawa Usman Sojaboy da wasu mata biyu shiga harkokin Film ko waka a Kano

January 20, 2025

Madrid ko Barca: Wa zai lashe Spanish Super Cup?

January 12, 2025

Barca ta kara rashin nasarar ɗaukaka kara kan yi wa Olmo rijista

December 31, 2024
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.