Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Yan Najeriya sun biya sama naira tiriliyan 2 a matsayin kuɗin fansa – NBS
Afrika

Yan Najeriya sun biya sama naira tiriliyan 2 a matsayin kuɗin fansa – NBS

December 18, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn

NBS ta ce an biya kuɗaɗen fansar ne tsakanin watan Mayu na shekarar 2023 zuwa watan Afrilun shekarar 2024.

Rahoton ya ƙara da cewa kashi 65 cikin 100 na gidajen da iftila’in garkuwa da mutane ya shafa sun biya kuɗin fansa domin a saki ‘yan’uwansu.

A rahoton da hukumar ta fitar ranar Talata game da laifuka da kuma yadda ake tafiyar da harkokin tsaro a Nijeriya, ta ce masu garkuwa da mutane sun kashe fiye da mutum 600,000 sannan suka sace fiye da mutum miliyan biyu a faɗin Nijeriya tsakanin watan Mayun 2023 zuwa Afrilun 2024.

“Matsaƙaicin kuɗin fansar da aka biya ya kai N2,670,693, yayin da jumullar kuɗin fansar da aka biya a lokacin ya kai N2,231,772,563,507,” kamar yadda rahoton NBS ya bayyana.

Rahoton ya ce garkuwa da mutane da aka yi a faɗin ƙasar ya kai 2,235,954 inda aka yi garkuwa da mutane sau 1,668,104 a karkara fiye da cikin birane inda aka yi sau 567,850.

“Idan aka yi la’akari da shiyyoyin da garkuwa da mutanen ya fi faruwa kuwa, za a ga cewa yankin arewa maso yammacin Nijeriya ne ya fi yawan garkuwa da mutane (1,420,307), inda arewa maso tsakiyar Nijeriya yake binsa (317,837), sannan kuma kudu maso gabashin Nijeriya ne na ƙarshe (110,432),” in ji hukumar.

Cikin iyalan da suka fuskanci garkuwa da mutane, rahoton ya nuna cewa kashi 80.5 cikin 100 sun sanar da ‘yan sanda.

“Shiyyar kudu masu kudun Nijeriya ce mutane suka fi sanar da mjutane cewa an yi garkuwa da ‘yan uwansu inda kashi 100 cikin 100 na wadanda abin ya shafa suka sanar da ‘yan sanda, yayin da shiyyar arewa maso tsakiyar Nijeriya ke binta da kashi 89.6 cikin 100 suka sanar da ‘yan sanda kuma arewa maso yammmacin Nijeriya ta zo ta ƙarshe inda kashi 73.9 cikin 100 suka sanar da ‘yan sanda,” kamar yadda rahoton ya bayyana.

“Idan kuma aka yi la’akari da inda mutane ke zaune kuma birane sun fi sanar da ‘yan sanda inda suka samu kashi 87.1 cikin 100 yayin da mutanen ƙauyuka suka sami kashi 77.3 cikin 100.”

Rahoton ya ƙara da cewa an kashe wasu daga cikin waɗanda aka yi garkuwa da su ɗin yayin da aka sake wasu daga cikinsu.

Ya nuna cewa daga cikin mutanen da aka ba da labarin cewa an yi garkuwa da su, an sake kashi 82.1 cikin 100, inda ka kashe kashi 12.8 cikin 100 yayin da har yanzu kashi 3.3 cikin 100 suna hannun masu garkuwa da mutane.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Kwalejin Ilimi ta Isa Kaita dake Karamar Hukumar Dutsenma a Jihar Katsina ta tuna da Marigayi Isa Kaita

July 2, 2025

Da gudu zan karɓi tayin kujerar mataimakin shugaban Najeriya – Barau I Jibrin

June 26, 2025

Babbar Kotun Tarayya ta yi umarni ga Hukumar EFCC data cigaba da bincike kan filin Musabaka da ake zargin wasu a Jihar Kano sun siyar ba bisa ka’ida ba

May 23, 2025

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta bayyana aniyarta na fara amfani da fasahar ƙirƙirarriyar basira ta AI wajen gudanar da ayyukan zaɓe a ƙasar

May 23, 2025

Gwamnatin jihar Kano ta kashe fiye da Naira Biliyan Biyu wajen karbo shidar kammala yan asalin Jihar karatun Dalibai Tamanin da Hudu

May 23, 2025

Gwamnatin jihar Kano ba zata lamunci Jan kafa ba wajen ajiye mutanen da ake tuhuma da laifi a gidan gyaran Hali

May 19, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Kano

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

By WafsymApril 13, 2025

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta bayana Dalilan yin Gwanjon…

Hukumar tace fina-finai ta haramtawa Usman Sojaboy da wasu mata biyu shiga harkokin Film ko waka a Kano

January 20, 2025

Madrid ko Barca: Wa zai lashe Spanish Super Cup?

January 12, 2025

Barca ta kara rashin nasarar ɗaukaka kara kan yi wa Olmo rijista

December 31, 2024
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.