Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » NiMet tayi hasashen samun ruwan sama mai haɗe da tsawa a faɗin Nijeriya
Afrika

NiMet tayi hasashen samun ruwan sama mai haɗe da tsawa a faɗin Nijeriya

September 23, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
rain
rain

Hukumar da ke kula da hasashen yanayi ta Nijeriya NiMet ta yi hasashen yuwar samun ruwa mai ɗauke da tsawa a faɗin kasar tun daga ranar Litinin, 23 ga Satumba zuwa Laraba 25.

Hasashen wanda NiMet ta fitar a ranar Lahadi ya nuna cewa za a samu ruwan sama da safiyar Litinin a jihohin Sokoto da Kebbi da Borno.

Haka kuma hukumar ta yi hasashen cewa akwai yiwuwar samun ruwan sama a Jigawa da Taraba da Adamawa da Gombe da Bauchi da Kano da Katsina da Kaduna da Zamfara da Kebi da Sokoto a ranar Litinin ɗin da rana.

“Akwai yiwuwar samun ruwan sama a wasu sassa na Abuja babban birnin Nijeriya da Neja da Nasarawa da Benue da Filato da Kwara da safe.

“Da rana da dare, ana sa ran samun ruwa a jihohin Kwara da Abuja da Neja da Benue da Kogi.

“Akwai yiwuwar samun ruwan da safe a kudu maso yammaci musamman a sassan Oyo da Ondo da Osun da Ekiti da Ogun har zuwa Legas da Delta da Ribas da Cross River da Akwa Ibom da Bayelsa da safe,” in ji hukumar.

Haka kuma NiMet ɗin ta ce da rana akwai yiwuwar samun ruwan saman a Enugu da Edo da Ebonyi da Ondo da Abia da Osun da Imo da Ekiti da Dekta da Bayelsa da Cross River da Ribas da Legas a ranar Litinin ɗin da rana.

An ta samun ruwan sama mai ƙarfi a ‘yan kwanakin nan a Nijeriyar lamarin da ya jawo ambaliyar ruwa a wasu sassan ƙasar wadda har ta kai ga asarar rayuka.

Ambaliyar dai ta fi ɓarna a ‘yan kwanakin nan a ƙasar ita ce wadda aka samu a birnin Maiduguri na jihar Borno dakr arewa maso gabashin Najeriya, inda aka yi asarar rayuka, gidaje da dukiyoyi mai tarin yawa.

Featured
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Kwalejin Ilimi ta Isa Kaita dake Karamar Hukumar Dutsenma a Jihar Katsina ta tuna da Marigayi Isa Kaita

July 2, 2025

Da gudu zan karɓi tayin kujerar mataimakin shugaban Najeriya – Barau I Jibrin

June 26, 2025

Hatsaniyar data Faru a Karamar Hukumar Rano wadda ta kai ga Rasuwar DPO da wani mutum daya– ‘Yan sanda Sun Nemi Hadin kai don Dawo da Tsaro a Yankin

May 27, 2025

Babbar kotun shariar musulunci ta yankewa matashin nan Shafiu Abubakar hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan samunsa da laifin kashe wasu mutane

May 27, 2025

Hukumar tace fina-finai ta yi nasarar kama wasu na’urori da ake amfani dasu wajan buga hotunan batsa ga masu sana’ar maganin Gargajiya a Jahar Kano

May 26, 2025

Babbar Kotun Tarayya ta yi umarni ga Hukumar EFCC data cigaba da bincike kan filin Musabaka da ake zargin wasu a Jihar Kano sun siyar ba bisa ka’ida ba

May 23, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Kano

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

By WafsymApril 13, 2025

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta bayana Dalilan yin Gwanjon…

Hukumar tace fina-finai ta haramtawa Usman Sojaboy da wasu mata biyu shiga harkokin Film ko waka a Kano

January 20, 2025

Madrid ko Barca: Wa zai lashe Spanish Super Cup?

January 12, 2025

Barca ta kara rashin nasarar ɗaukaka kara kan yi wa Olmo rijista

December 31, 2024
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.