Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Da sanina ko da gangan bazan zubar da mutuncina ba kuma bazan baku kunya ba – Sabon Shugaban NAHCON Farfesa Pakistan
Afrika

Da sanina ko da gangan bazan zubar da mutuncina ba kuma bazan baku kunya ba – Sabon Shugaban NAHCON Farfesa Pakistan

August 25, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
WhatsApp Image 2024 08 25 at 16.25.49
WhatsApp Image 2024 08 25 at 16.25.49

Sabon shugaban hukumar Alhazan Nigeria NAHCON Farfesa Abdullahi Saleh Usman Pakistan, ya ci alwashin yin aiki tukuru domin tabbatar da gudanar da aiki mai tsafta tare da kawo cigaba a hukumar.

‘’Tafiyar da hukumar alhazan Najeriya NAHCON aiki ne mai girman gaske dake bukatar tayani da addu’a domin na samu karfin gwiwar tafiyar da aikin cikin gaskiya da amana” inji Farfesa Pakistan.

Shugaban hukumar ta NAHCON na wannan jawabin ne lokacin da gidauniyar cigaban Tudun Murtala dake jihar Kano a arewacin kasar ta kai masa ziyarar taya murna gidansa, bisa mukamin da shugaban kasar Bola Ahmed Tinubu ya bashi na suhagabantar hukumar alhazan NAHCON.

Yayin ziyayar, Farfesa Muhammad Binyamin Ado da Dagacin Dakata Alhaji Salisu Ibrahim sun bayyana cewa kujerar shugabancin NAHCON bata taba zuwa jihar Kano ba, saboda haka akwai bukatar taya Farfesa Pakistan murana da addu’ar samun ikon sauke nauyin al’ummar Najeriya.

“A matsayinka na dan Tudun Murtala kuma Allah ya baka wannan mukami, ya zama wajibi muzo a kungiyance mutayaka murna muyi maka fatan alkhairi” Injin Farfesa Muhammd Binyamin.

Lokacin da shugaban gidauniyar cigaban al’ummar Tudun Murtala Alhaji Yahya Umar Bagobiri ke nasa jawabin, godewa shugaban Nigeria Tinubu da Mataimakinsa Kashim Shatima yayi bisa dora kwarya a gurbinta.

‘’Dole na godewa shugaban Nigeria Bola Tinubu da mataimakin Kashim Shattima bisa wannan babbar kujera daka bawa dan Tudun Murtala, kujerar da bata taba zuwa jihar Kano balle kuma wannan gari namu ba. Inji Yahaya Bagobiri

Shugaban hukumar ta NAHCOON Farfesa Abdullah Saleh Pakistan yayi alkawarin cewa ba zai bawa malamai da sauran al’umma kunya ba, bisa wannan nauyi da shugaban kasa ya dora masa.

‘’Tunda kuna ce min malam, ina mai tabbatar muku cewa da Sanina ko dagangan, bazan zubar da mutuncina ba kuma bazan taba baku kunya ba, domin duk abinda nayi mara kyau sai ya shafi wannan unguwa ta Tudun Murtala, domin babu abinda wannan gari na karramawa wanda baiyimin ba”Inji Shugaban na NAHCON.

Manyan mutane daga unguwar ciki hadda Farfesa Atiku da masu unguwanni, limamai da sauran al’ummar garin ne suka halarci ziyarar taya sabon shugaban hukumar ta NAHCOON Farfesa Abdullahi Saleh Usman Pakistan Murna.

Featured
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Za mu mayar da martani kan harin da aka kai wa jirgin ruwanmu – Koriya ta Kudu

May 11, 2026

Dalilin da ya sa na maida akwatin zaɓena Abuja – Pantami

May 11, 2026

Dangote na shirin gina matatar mai a ƙasar Kenya

May 11, 2026

Samar da Aminci, Shi Ne Farko — Dole a Kawar Da Siyasar Dauka Makamai Daga Fagen Siyasar Kano

May 5, 2026

Pantami ya yi watsi da tsarin maslaha bayan kin daukar shi a matsayin dan takarar gwamnan Gombe

May 3, 2026

Kwankwaso da Obi sun koma jam’iyyar NDC

May 3, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.