Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Sabon shugaban Iran yana neman hanyar sasantawa da ƙasashen duniya biyo bayan mayar da ƙasar saniyar ware.
Asia

Sabon shugaban Iran yana neman hanyar sasantawa da ƙasashen duniya biyo bayan mayar da ƙasar saniyar ware.

August 23, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
iran2
iran2

A ranar 11 ga watan Agusta ne, sabon zaɓaɓɓen shugaban na Iran Masoud Pezeshkian ya gabatar da sunayen mutanen da yake so a ba ministoci a gaban majalisar dokokin ƙasar domin neman ƙuri’ar amincewa.

Dangane da dokar Iran, kakakin majalisar ƙasar zai karanta takardar gabatarwa ta shugaban ƙasar, inda bayan haka sai sauran takardu su biyo baya waɗanda za a miƙa su ga kwamitocin da suka dace domin dubawa.

Waɗannan kwamitocin an kafa su ne domin tantance cancanta da takardu da asali da kuma shawarar bayar da ma’aikatar da ta dace ga kowane minista tare da gabatar da bincikensu ga kakakin majalisa. Haka kuma za a buga takardun wannan rahoto tare da miƙa su ga duka mambobin majalisa domin bitarsu.

Mako ɗaya bayan gabatarwar ta gwamnati, za a yi zama daban-daban a majalisa domin tafka muhawara dangane da tsare-tsare da shirye-shirye na gwamnati tare da gudanar da ƙuri’ar amincewa dangane da ministocin.

A cikin wannan lokacin, ministocin da aka zaɓe su za su aika da shirye-shiryensu ga kwamitocin da suka dace da kuma mayar da martani dangane da duk wata buƙata daga mambobin kwamitin.

Ana saran matakin zai kai ga samun kuri’un amincewa da kowane minista, sannan kuma za a kada kuri’ar amincewa ga daukacin majalisar ministocin kasar.

Majalisar ministocin da Pezeshkian ke son ya kafa

Gabatar da sunayen ministoci da shugaban ya yi ya jawo zazzafar muhawara a kafofin watsa labarai na Iran, inda akasarinsu suke mayar da hankali dangane ko yanayin waɗanda aka zaɓa a ministoci ya zo daidai da alƙawarin da Pezeshkian ya yi a lokacin yaƙin neman zaɓe dangane da irin mutanen da zai yi aiki da su.

Musamman ma, matsakaitan shekarun mambobin majalisar ministocin ya kai kusan shekara 60. Mace daya ce kawai aka zaba, kuma majalisar ministocin kasar mai rinjayen ‘yan Shi’a ba ta da wakilcin ‘yan Sunna.

Idan aka yi la’akari da manyan kalaman da ya rinƙa yi dangane da batun kawo sauyi, da alama majalisar ministocin da ake son kafawa ta yi kama da mai matsakaicin ra’ayi, ta karkata ga ra’ayin mazan jiya maimakon wacce aka yi alkawarin kawo sauyi.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Kwalejin Ilimi ta Isa Kaita dake Karamar Hukumar Dutsenma a Jihar Katsina ta tuna da Marigayi Isa Kaita

July 2, 2025

Da gudu zan karɓi tayin kujerar mataimakin shugaban Najeriya – Barau I Jibrin

June 26, 2025

Babbar Kotun Tarayya ta yi umarni ga Hukumar EFCC data cigaba da bincike kan filin Musabaka da ake zargin wasu a Jihar Kano sun siyar ba bisa ka’ida ba

May 23, 2025

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta bayyana aniyarta na fara amfani da fasahar ƙirƙirarriyar basira ta AI wajen gudanar da ayyukan zaɓe a ƙasar

May 23, 2025

Gwamnatin jihar Kano ta kashe fiye da Naira Biliyan Biyu wajen karbo shidar kammala yan asalin Jihar karatun Dalibai Tamanin da Hudu

May 23, 2025

Gwamnatin jihar Kano ba zata lamunci Jan kafa ba wajen ajiye mutanen da ake tuhuma da laifi a gidan gyaran Hali

May 19, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Kano

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

By WafsymApril 13, 2025

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta bayana Dalilan yin Gwanjon…

Hukumar tace fina-finai ta haramtawa Usman Sojaboy da wasu mata biyu shiga harkokin Film ko waka a Kano

January 20, 2025

Madrid ko Barca: Wa zai lashe Spanish Super Cup?

January 12, 2025

Barca ta kara rashin nasarar ɗaukaka kara kan yi wa Olmo rijista

December 31, 2024
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.