Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Dandazon jama’a sun tarbi Gwamna Yusuf a Kano 
Afrika

Dandazon jama’a sun tarbi Gwamna Yusuf a Kano 

April 5, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
1775355352541

Dubban al’ummar jihar Kano sun fito kan tituna a ranar Asabar domin tarbar Gwamna Abba Yusuf bayan dawowarsa daga Abuja, inda ya gana da shugabannin jam’iyyar APC.

Rahotanni sun nuna cewa gwamnan ya kuma kasance cikin tawagar APC da ta je jihar Bauchi domin jawo Gwamna Bala Mohammed ya koma jam’iyyar daga PDP, duk da cewa har yanzu bai bayyana matsayinsa ba.

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

Tarbar ta biyo bayan sauye-sauyen siyasa a Kano, ciki har da ficewar Rabiu Musa Kwankwaso daga NNPP zuwa ADC tare da hadewa da Peter Obi da sauran ‘yan adawa.

Magoya bayan Yusuf sun cika tituna daga filin jirgin sama na Malam Aminu Kano zuwa gidan gwamnati, suna daga tutoci tare da rera wakokin goyon baya, lamarin da ya haifar da yanayi irin na shagali.

Wasu mazauna Kano sun bayyana tarbar a matsayin daya daga cikin mafi girma a baya-bayan nan, suna mai cewa hakan na nuna karfin goyon bayan da gwamnan ke da shi a kasa.

Masu sharhi kan siyasa sun ce sauye-sauyen da ke gudana, musamman sauyin da Kwankwaso ya yi, sun kara tsananta adawar siyasa a Kano, wadda ke da muhimmanci wajen zaben shugaban kasa a Najeriya.

Wasu mazauna Kano sun kuma nuna cewa wannan goyon baya zai bayyana a zaben 2027, inda suka yi alkawarin mara wa Yusuf baya domin ci gaba da ayyukansa.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

‘Ba zan ba ‘yan Najeriya kunya ba’ – Shugaba Tinubu

April 17, 2026

Wannan ce takarata ta ƙarshe – Atiku

April 15, 2026

Shekaru 12 bayan sace ƴan matan Chibok

April 15, 2026

Tsagin ADC ƙarƙashin David Mark ya kori Nafiu Bala da wasu bisa zargin yi wa jam’iyya zagon-ƙasa

April 15, 2026

Hukumomin yaƙi da cin hanci ba su taɓa gayyata ta ba — Pantami

April 14, 2026

An kama jami’an ƴansanda 6 tare da wasu mutane 3 bisa zargin ƙwace da satar mutane a Edo 

April 14, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

By WafsymApril 2, 2026

A Jihar Kano, ana ci gaba da nuna damuwa kan yadda wasu masu anfani da…

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.