Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Gwamnatin Kano Za Ta Tallafa Wa duk Wani Yunkurin Da Zai Kawar Da Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi A Jihar 
Kano

Gwamnatin Kano Za Ta Tallafa Wa duk Wani Yunkurin Da Zai Kawar Da Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi A Jihar 

September 9, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
IMG 20260909 WA0035

Gwamnatin Jihar Kano ta ce a shirye take ta tallafa wa duk wani yunkuri da zai taimaka wajen kawar da matsalar ta’ammali da miyagun ƙwayoyi a jihar.

Kwamishinan Lafiya na jihar, Dr Abubakar Labaran Yusuf, ne ya bayyana hakan a yayin ƙaddamar da gidauniyar The Recovery Hub, wadda aka kafa domin taimaka wa masu fama da matsalar shaye-shaye da kuma wayar da kan al’umma kan illolin miyagun ƙwayoyi.

Kwamishinan ya ce gwamnatin jihar ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf, na ɗaukar matsalar shaye-shaye da matuƙar muhimmanci, saboda illar da take haifarwa ga lafiyar al’umma, musamman matasa.

Ya ce gwamnati za ta ci gaba da tallafa wa shirye-shirye da ƙungiyoyin da ke da manufar yaƙi da shaye-shaye, tare da haɗa hannu da hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki domin dakile matsalar.

“Gwamnati a shirye take ta taimaka wa duk wani yunkuri da zai taimaka wajen kawar da ta’ammali da miyagun ƙwayoyi,” in ji kwamishinan.

Ya jaddada muhimmancin haɗin gwiwa tsakanin gwamnati, hukumomin tsaro, ƙwararrun ma’aikatan lafiya, ƙungiyoyin fararen hula da al’umma wajen samun nasara a yaƙi da matsalar.

A nasa jawabin, Shugaban gidauniyar The Recovery Hub, Dr Abdullahi Akilu, wanda likitan ƙwaƙwalwa ne a Asibitin Dawanau da ke Kano, ya nuna damuwa kan yadda matsalar shaye-shayen miyagun ƙwayoyi ke ƙara yaɗuwa a tsakanin al’umma.

Dr Akilu ya ce an kafa gidauniyar ne domin wayar da kan jama’a kan illolin shaye-shaye, da kuma samar da tallafi da kulawa ga mutanen da ke fama da matsalar.

Ya ce gidauniyar za ta kuma taimaka wa waɗanda suka samu sauƙi daga shaye-shaye wajen farfaɗowa da komawa cikin al’umma.

A cewarsa, matsalar miyagun ƙwayoyi ta zama babbar barazana ga al’umma, don haka ake buƙatar haɗin gwiwar gwamnati da hukumomi da sauran masu ruwa da tsaki domin magance ta.

Shi ma Shugaban Kwamitin Haɗin Gwiwar Hukumomin Jihar Kano kan Yaƙi da Shan Miyagun Ƙwayoyi da Fataucin Haramtattun Abubuwa, Muhuyi Magaji Rimingado, ya ce kwamitin zai yi aiki tare da The Recovery Hub domin ƙara ƙaimi wajen yaƙi da matsalar.

Muhuyi ya ce haɗin gwiwar hukumomi da ƙungiyoyin da ke taimaka wa masu fama da shaye-shaye na da matuƙar muhimmanci wajen rage matsalar da kuma kare matasa daga faɗawa cikin tarkon miyagun ƙwayoyi.

Ya yi kira ga iyaye da malamai da shugabannin al’umma da su ƙara ƙoƙari wajen wayar da kan matasa kan illolin shaye-shaye.

Taron ƙaddamar da gidauniyar ya samu halartar wakilan hukumomin tsaro da dama, da ƙungiyoyin lafiya, likitoci da sauran masu ruwa da tsaki. Daga cikin mahalarta akwai wakilan Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA), Rundunar ’Yan Sandan Najeriya, manyan likitoci daga Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano, wakilan Asibitin Dawanau da kuma Ƙungiyar Likitocin Najeriya (NMA).

Haka kuma, wakilan ƙungiyoyin fararen hula, ciki har da Youth Awareness Against Drug Abuse Initiative da Yan Jarida sun halarci taron, inda aka jaddada muhimmancin haɗin gwiwar hukumomi da ƙungiyoyi wajen yaƙi da matsalar shaye-shaye da wayar da kan al’umma, musamman matasa, samar da kulawa ga masu fama da matsalar da kuma taimaka musu wajen komawa cikin al’umma.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Kotu Ta Yanke Wa Mutane Biyu Daurin Shekaru 9 Kan Bai Wa Yara Kanana Kayan Shaye-shaye

September 8, 2026

Jam’iyyar Labour Party Ta Yi Alkawarin Kafa Hukumar Kula da Hayar Gidaje A Kano 

September 5, 2026

Kano PHCMB Ta Nemi Haɗin Kan Al’umma Don Inganta Kiwon Lafiya

August 18, 2026

Babu Mafaka Ga Masu Safarar Miyagun Ƙwayoyi A Kano — Muhyi Magaji

August 11, 2026

Sarkin Gaya: Mallakar Katin Zaɓe Shi Ne Ginshiƙin Zaɓen Shugabanni Nagari

July 3, 2026

Sahihin ‎Labari Ke Tabbatar Da Amincewar Jama’a, Ba Gaggawar Wallafa Ba- Shugaban NUJ

July 1, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Gwamnatin Kano Ta Yi Alƙawarin Ƙara Wa NDLEA Motoci Don Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ‎

June 29, 20267

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.