Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Rasuwar Ugboaja Ta Bar Babban Gibi A Ƙungiyar Ƙwadago — Abbas
Labaran Cikin Gida

Rasuwar Ugboaja Ta Bar Babban Gibi A Ƙungiyar Ƙwadago — Abbas

August 27, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
images 2026 08 27T153701.216

Ɗan takarar mataimakin gwamnan Jihar Kano na Jam’iyyar Labour Party (LP), Kwamared Abbas Ibrahim, ya bayyana rasuwar Babban Sakataren Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya (NLC), Kwamared Emmanuel Ugboaja, a matsayin babban rashi ga ƙungiyar ƙwadago da ma Najeriya baki ɗaya.

A cikin saƙon ta’aziyyar da ya aike wa Shugaban NLC, Kwamared Joe Ajaero, ranar 27 ga Agusta, 2026, Abbas ya ce rasuwar Ugboaja ta girgiza harkar ƙwadago, duba da irin gudunmawar da marigayin ya bayar wajen kare haƙƙin ma’aikata da inganta walwalarsu.

Ya ce marigayin ya kasance jagora mai hangen nesa wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen tabbatar da adalci da kare muradun ma’aikatan Najeriya.

Abbas ya ce ƙwarewar Ugboaja a fannin shari’a ta taimaka matuƙa wajen ƙarfafa gwagwarmayar ƙungiyar ƙwadago da kuma kare muradun ma’aikata a lokuta da dama.

Ya tuna da haɗuwarsa da marigayin a ɗaya daga cikin tarukan horaswa na NLC na Harmattan School, inda ya ce kalaman ƙarfafawa da shawarwarin da ya bayar suka yi tasiri ga mahalarta taron.

“Ko da yake Ugboaja ya riga mu gidan gaskiya, amma ya bar tarihi mai kyau da kuma abubuwan tunawa da za su ci gaba da kasancewa a zukatan waɗanda suka yi hulɗa da shi,” in ji Abbas.

Tsohon Mataimakin Sakataren NLC na Jihar Kano ya buƙaci shugabannin ƙungiyar da mambobinta su yi haƙuri tare da ci gaba da tafiya a kan manufofin da marigayin ya tsaya kai da fata wajen ganin an cimma su.

Ya kuma miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan marigayin, abokan aikinsa da daukacin al’ummar ƙwadago, tare da addu’ar Allah Ya gafarta masa kurakuransa, Ya sanya shi a Aljannatul Firdausi, sannan Ya bai wa iyalansa da abokan aikinsa juriyar wannan babban rashi.

Abbas, wanda kuma tsohon Shugaban Majalisar Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Najeriya (NUJ) reshen Jihar Kano ne, ya ce rasuwar Ugboaja ta haifar da wani gibi da zai yi wuya a cike a harkar ƙwadago ta ƙasar nan.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Allah Ya yi wa Alhaji Sani Gwarzo, wanda aka fi sani da “Tumbuleke”, rasuwa.

August 11, 2026

Gwamna Abba Ya Kaddamar da Kwamitin Yaƙi da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi, Ya Sanya Hannu Kan Dokar Daba A Kano

July 22, 2026

“Rikicin Shaidar Zama Ɗan Ƙasa a Jos North Ya Ɗauki Sabon Salo, Sarakunan Gargajiya Sun Nemi Shiga Cikin Shari’a.”

July 11, 2026

Sahihin ‎Labari Ke Tabbatar Da Amincewar Jama’a, Ba Gaggawar Wallafa Ba- Shugaban NUJ

July 1, 2026

NWUK Expels 34 Students Over Examination Malpractice

June 30, 2026

Gwamnatin Kano Ta Yi Alƙawarin Ƙara Wa NDLEA Motoci Don Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ‎

June 29, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Gwamnatin Kano Ta Yi Alƙawarin Ƙara Wa NDLEA Motoci Don Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ‎

June 29, 20267

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.